• English
  • Business News
Saturday, May 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Bankuna 5 Da Suka Samu Ribar Naira Tiriliyan 17.3 A Nijeriya

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
3 weeks ago
in Labarai
0
Manyan Bankuna 5 Da Suka Samu Ribar Naira Tiriliyan 17.3 A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Duk da tulin matsalolin tattalin arziki da ake fuskanta, manyan bankuna gudana biyar a Nijeriya sun samu gagarumin ribar na naira tiriliyan 5.1 a shekarar 2024, wato kaso 59.4 cikin 100 daga na shekarar 2023 da aka samu naira tiriliyan 3.2.

 

Manyan bankuna biyar wadanda suka hada da First HoldCo, United Bank for Africa (UBA), GTCO, Access Holdings da kuma Zenith Bank, akasari sun samo ribar ne sakamakon yawan kudin ruwa da aka samu, da sake farfado da canjin kudaden waje da kuma karuwar kudaden shiga maras riba.

  • An Sako Malamin Kiristan Cocin Katolika Da Aka Sace A Kaduna
  • Idan Kana Son Barin PDP, Yanzu Ne Lokacin – Bukola Saraki

Baya ga haka, hada-hadar kudaden da manyan bankunan biyar suka samu ya tashi daga naira tiriliyan 9.6 a shekarar 2023 zuwa naira tiriliyan 17.3 a bara, wanda ya nuna karuwar kashi 80 cikin 100.

 

Labarai Masu Nasaba

Mutum 3 Sun Rasu, Wasu Sun Jikkata Yayin Da Bama-bamai Suka Tashi A Hanyar Borno

Hukuma Ta Haramta Bikin Ranar Kauyawa A Kano

Bankin Zenith ya kasance a kan gaba tare da samun ribar naira tiriliyan 1.32 kafin a biya haraji, wanda hakan ke nuna karin kashi 67 cikin 100 daga naira biliyan 796 da aka samu a shekarar 2023.

 

Bankin GTCO ya bi sahu, inda ya fitar da ribar kashi 107.8 kafin a fara biyan haraji zuwa naira tiriliyan 1.266, daga naira biliyan 609 na bara.

 

Har ila yau, Access Corp da UBA sun taka rawar gani sosai, inda suka samu ribar naira biliyan 867 da kuma naira biliyan 803.7, wanda ya zarce adadin da suka samu a shekarar 2023 na naira biliyan 729 da kuma naira biliyan 757.6.

 

First HoldCo ya kuma samu ribar kashi 124 cikin 100 na ribar da aka samu, daga naira biliyan 347.9 a shekarar 2023 zuwa naira biliyan 781.9 a shekarar da ta gabata.

 

Masu gudanarwa sun yi amanar cewa juriyar da fannin banki ke nunawa ba wai kawai shaida ce ga daidaitawar cibiyoyin hada-hadar kudi ba har ma da nunin damar da za a samu nan gaba, musamman ga masu saka hannun jari da ke sa ran samun kwanciyar hankali.

 

Ko da yake sun bayar da hujjar cewa, idan aka yi hasashen farashin kudin ruwa zai ragu, kuma nairar za ta kara karfi tare da rage sauyin yanayi, ribar bankunan na iya fuskantar matsin lamba a bana.

 

Duk da haka, kwararrun sun ci gaba da jajircewa kan fannin, tare da lura da cewa bankunan da ke da kakkarfan habakar lamuni da kuma dabarun samun kudin shiga maras riba, musamman wadanda ke yin amfani da ayyukan kasuwanci, da alama za su kasance masu jan hankali ga masu zuba jari.

 

Wani manazarci, Charles Abuede, ya ce ayyukan bankunan Nijeriya a cikin shekara ta 2024 suna ba da manuniya mai kyau ga abin da ke gaba a 2025.

 

Ya ce, akwai hasashen za a samu karin tagomashi sosai a bangarorin a shekarar bana, wanda a cewarsu ayyukan na kyau matuka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Fita Daga PDP: Babu Wani Abu Da Zai Cutar Da PDP, Jam’iyyarmu Za Ta Ƙara Haɓaka – Bukola Saraki

Next Post

Rahoton Gwamnatin Amurka Game Da Shawo Kan Yaduwar Makamai Tamkar Ba’a Amurkan Ta Yiwa Kanta

Related

Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno
Manyan Labarai

Mutum 3 Sun Rasu, Wasu Sun Jikkata Yayin Da Bama-bamai Suka Tashi A Hanyar Borno

4 hours ago
Hukuma Ta Haramta Bikin Ranar Kauyawa A Kano
Labarai

Hukuma Ta Haramta Bikin Ranar Kauyawa A Kano

6 hours ago
Dalilin Ƴansandan Kano Na Tsare Wasu Awaki
Labarai

Dalilin Ƴansandan Kano Na Tsare Wasu Awaki

8 hours ago
Ƙungiyar Fulani Makiyaya Ta Nuna Damuwarta Na Ɓacewar Mataimakin Shugabanta
Labarai

Ƙungiyar Fulani Makiyaya Ta Nuna Damuwarta Na Ɓacewar Mataimakin Shugabanta

9 hours ago
Hisbah Ta Rufe Otal, Ta Kwato Ƙwalaben Giya 209 A Yobe
Labarai

Hisbah Ta Rufe Otal, Ta Kwato Ƙwalaben Giya 209 A Yobe

10 hours ago
Babu Wani Dan Jarida Da Aka Hana Shiga Taron Gwamnonin Arewa – CPS Ibrahim Musa
Labarai

Babu Wani Dan Jarida Da Aka Hana Shiga Taron Gwamnonin Arewa – CPS Ibrahim Musa

11 hours ago
Next Post
Rahoton Gwamnatin Amurka Game Da Shawo Kan Yaduwar Makamai Tamkar Ba’a Amurkan Ta Yiwa Kanta

Rahoton Gwamnatin Amurka Game Da Shawo Kan Yaduwar Makamai Tamkar Ba’a Amurkan Ta Yiwa Kanta

LABARAI MASU NASABA

Masana Kimiyya Na Kasar Sin Sun Gano Wata Sabuwar Hallita A Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar 

Masana Kimiyya Na Kasar Sin Sun Gano Wata Sabuwar Hallita A Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar 

May 17, 2025
Crystal Palace Ta Lashe Kofin FA Karon Farko, Ta Doke Manchester City 1-0

Crystal Palace Ta Lashe Kofin FA Karon Farko, Ta Doke Manchester City 1-0

May 17, 2025
Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 17, 2025
Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taro Na 34 Na Kasashen Larabawa

Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taro Na 34 Na Kasashen Larabawa

May 17, 2025
Jami’ar FUDMA Ta Ƙara Fadawa Cikin Rikicin Shuagabanci A Katsina

Jami’ar FUDMA Ta Ƙara Fadawa Cikin Rikicin Shuagabanci A Katsina

May 17, 2025
Rokar Kasuwanci Ta Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 6 Zuwa Sararin Samaniya

Rokar Kasuwanci Ta Kasar Sin Ta Harba Taurarin Dan Adam 6 Zuwa Sararin Samaniya

May 17, 2025
Gidan Adana Kayayyakin Tarihi Na Amurka Ya Mayarwa Kasar Sin Rubuce-rubucen Hannu Masu Daraja Na Lokacin Yake-yake A Kasar

Gidan Adana Kayayyakin Tarihi Na Amurka Ya Mayarwa Kasar Sin Rubuce-rubucen Hannu Masu Daraja Na Lokacin Yake-yake A Kasar

May 17, 2025
Bude Kofar Kasar Sin Dama Ce Ga Duniya Har Abada

Bude Kofar Kasar Sin Dama Ce Ga Duniya Har Abada

May 17, 2025
Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno

Mutum 3 Sun Rasu, Wasu Sun Jikkata Yayin Da Bama-bamai Suka Tashi A Hanyar Borno

May 17, 2025
Hukuma Ta Haramta Bikin Ranar Kauyawa A Kano

Hukuma Ta Haramta Bikin Ranar Kauyawa A Kano

May 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.