ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fita Daga PDP: Babu Wani Abu Da Zai Cutar Da PDP, Jam’iyyarmu Za Ta Ƙara Haɓaka – Bukola Saraki

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
PDP

Tsohon shugaban majalisar dattawan Nijeriya kuma Wazirin masarautar Ilorin, Dr. Abubakar Bukola Saraki, ya bayyana cewa; bayan ficewar gwamnan jihar Delta daga jam’iyyar PDP zuwa APC, ina ta samun kiran waya daga shugabanni da ƴan jam’iyya matasa da maza da mata, waɗanda suka tsaya tsayin daka wajen ganin an samu ci gaban dimokuraɗiyya.

Yawancin masu kiran waya suna son su ji matsayata a kan fitar gwamnan jihar Delta da ƴan tawagarsa.

  • Wasanni Na Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Ci Gaban Matasa — Gidauniyar Bukola Saraki 
  • Kotu Ta Wanke Tsohon Dogarin Bukola Saraki Kan Zargin Biliyan ₦3.5b

Matsaya ta akan wannan magana shi ne, waɗanda ke son barin PDP su fita tun yanzu, su bar sauran da ke son ci gaba, mu mayar da hankali wajen sake gina jam’iyyar.

ADVERTISEMENT

Yana da muhimmanci duk ɗan Nigeriya ya sani cewa dole ne a tashi tsaye wajen tabbatar da dimokuraɗiyya. Domin tabbatar da hakan, dole ne a samu jam’iyyu masu ƙarfi domin tursasa gwamnati ta yi abin da ya kamata.

Maganar zama jam’iyya ɗaya a ƙasar nan ba abu bane wanda zai zama alheri kasancewar ƙasa ce mai addinai daban-daban da ƙabilu daban-daban da yare daban-daban. Ai abin tsoro ne ma a ce a zauna babu wasu jam’iyyu sai jam’iyya ɗaya, hakan zai nuna cewa mutane ba su da zaɓi, duk abin da aka ga dama shi za a yi musu.

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Saboda haka akwai buƙatar duk wani ɗan ƙasa ya tsaya tsayin daka wajen ganin an samu jam’iyyar adawa mai ƙarfi, wadda za ta karɓi mulki daga hannun jam’iyya mai mulki.

Saƙona ga ƴan jam’iyya shi ne duk wanda yake son ya tafi ga hanya nan, wanda yake son gyara kuma ya zauna a gyara domin mu samu mutane masu amana, waɗanda za mu dinga rufe ƙofa da su kuma ba za su fitar da maganar a waje ba.

Halin da ake ciki yanzu ya bayyana irin matsayar da mutane irina suke kai tun farko na yin shiru domin ganin yadda abubuwa suke tafiya. Tabbas na yadda cewa babu gaskiya a wajen wasu shugabannin daga jam’iyya mai mulki domin yanzu baka san da wa zaka amince kayi maganar sirri ba.

Ya zama dole ƴan jam’iyyar PDP su daina zargin jam’iyya mai mulki da kawo rikici a PDP, domin hakan nuna gazawa ne domin kowa yana yin yadda zai yi ne domin ya samu nasara a zaɓe. Saboda haka ya zama dole a san abin yi, a yi aiki tuƙuru wajen kawo gyara a jam’iyyar PDP.

Tabbas akwai takaici a ce mataimakin ɗan takarar shugaban ƙasa a zaɓen da ya gabata ya fice daga jam’iyya ya koma jam’iyya mai mulki, babu wanda zai gaya maka wani dalilii mai ƙarfi na yin hakan. Kawai hakan yana nuna rashin manufa ne da yadda muka lalace a siyasance.

Tun farko daman shi ne dalilin da yasa nake yawan cewa mu ƙarfafa tsarin mulki da hukumomi a kan ƙarfafa wani mutum guda ɗaya. Duk da fitar gwamnan jihar Delta, har yanzu muna da damar cin zaɓe a ƙasar nan.

Ƴan jam’iyyar mu ya kamata su nutsu, su samu ƙwarin gwiwa domin samun nasara. Mu kalli wannan halin da muke ciki a matsayin wani darasi da zai sa mu sake gina jam’iyyarmu. Akwai nasara a nan gaba

Ina da tabbacin cewa nan ba da jimawa ba shugabancin jam’iyya a matakai daban-daban zai sake zama domin tattauna halin da ake ciki da kawo mafita. Saboda haka babu tashin hankali a cikin abin da ke faruwa.

PDP
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Manyan Bankuna 5 Da Suka Samu Ribar Naira Tiriliyan 17.3 A Nijeriya

Manyan Bankuna 5 Da Suka Samu Ribar Naira Tiriliyan 17.3 A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.