ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fita Daga PDP: Babu Wani Abu Da Zai Cutar Da PDP, Jam’iyyarmu Za Ta Ƙara Haɓaka – Bukola Saraki

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
PDP

Tsohon shugaban majalisar dattawan Nijeriya kuma Wazirin masarautar Ilorin, Dr. Abubakar Bukola Saraki, ya bayyana cewa; bayan ficewar gwamnan jihar Delta daga jam’iyyar PDP zuwa APC, ina ta samun kiran waya daga shugabanni da ƴan jam’iyya matasa da maza da mata, waɗanda suka tsaya tsayin daka wajen ganin an samu ci gaban dimokuraɗiyya.

Yawancin masu kiran waya suna son su ji matsayata a kan fitar gwamnan jihar Delta da ƴan tawagarsa.

  • Wasanni Na Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Ci Gaban Matasa — Gidauniyar Bukola Saraki 
  • Kotu Ta Wanke Tsohon Dogarin Bukola Saraki Kan Zargin Biliyan ₦3.5b

Matsaya ta akan wannan magana shi ne, waɗanda ke son barin PDP su fita tun yanzu, su bar sauran da ke son ci gaba, mu mayar da hankali wajen sake gina jam’iyyar.

ADVERTISEMENT

Yana da muhimmanci duk ɗan Nigeriya ya sani cewa dole ne a tashi tsaye wajen tabbatar da dimokuraɗiyya. Domin tabbatar da hakan, dole ne a samu jam’iyyu masu ƙarfi domin tursasa gwamnati ta yi abin da ya kamata.

Maganar zama jam’iyya ɗaya a ƙasar nan ba abu bane wanda zai zama alheri kasancewar ƙasa ce mai addinai daban-daban da ƙabilu daban-daban da yare daban-daban. Ai abin tsoro ne ma a ce a zauna babu wasu jam’iyyu sai jam’iyya ɗaya, hakan zai nuna cewa mutane ba su da zaɓi, duk abin da aka ga dama shi za a yi musu.

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Saboda haka akwai buƙatar duk wani ɗan ƙasa ya tsaya tsayin daka wajen ganin an samu jam’iyyar adawa mai ƙarfi, wadda za ta karɓi mulki daga hannun jam’iyya mai mulki.

Saƙona ga ƴan jam’iyya shi ne duk wanda yake son ya tafi ga hanya nan, wanda yake son gyara kuma ya zauna a gyara domin mu samu mutane masu amana, waɗanda za mu dinga rufe ƙofa da su kuma ba za su fitar da maganar a waje ba.

Halin da ake ciki yanzu ya bayyana irin matsayar da mutane irina suke kai tun farko na yin shiru domin ganin yadda abubuwa suke tafiya. Tabbas na yadda cewa babu gaskiya a wajen wasu shugabannin daga jam’iyya mai mulki domin yanzu baka san da wa zaka amince kayi maganar sirri ba.

Ya zama dole ƴan jam’iyyar PDP su daina zargin jam’iyya mai mulki da kawo rikici a PDP, domin hakan nuna gazawa ne domin kowa yana yin yadda zai yi ne domin ya samu nasara a zaɓe. Saboda haka ya zama dole a san abin yi, a yi aiki tuƙuru wajen kawo gyara a jam’iyyar PDP.

Tabbas akwai takaici a ce mataimakin ɗan takarar shugaban ƙasa a zaɓen da ya gabata ya fice daga jam’iyya ya koma jam’iyya mai mulki, babu wanda zai gaya maka wani dalilii mai ƙarfi na yin hakan. Kawai hakan yana nuna rashin manufa ne da yadda muka lalace a siyasance.

Tun farko daman shi ne dalilin da yasa nake yawan cewa mu ƙarfafa tsarin mulki da hukumomi a kan ƙarfafa wani mutum guda ɗaya. Duk da fitar gwamnan jihar Delta, har yanzu muna da damar cin zaɓe a ƙasar nan.

Ƴan jam’iyyar mu ya kamata su nutsu, su samu ƙwarin gwiwa domin samun nasara. Mu kalli wannan halin da muke ciki a matsayin wani darasi da zai sa mu sake gina jam’iyyarmu. Akwai nasara a nan gaba

Ina da tabbacin cewa nan ba da jimawa ba shugabancin jam’iyya a matakai daban-daban zai sake zama domin tattauna halin da ake ciki da kawo mafita. Saboda haka babu tashin hankali a cikin abin da ke faruwa.

PDP
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
  • Abba Ibrahim Wada
    FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
  • Abba Ibrahim Wada
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Manyan Bankuna 5 Da Suka Samu Ribar Naira Tiriliyan 17.3 A Nijeriya

Manyan Bankuna 5 Da Suka Samu Ribar Naira Tiriliyan 17.3 A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.