ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Fita Daga PDP: Babu Wani Abu Da Zai Cutar Da PDP, Jam’iyyarmu Za Ta Ƙara Haɓaka – Bukola Saraki

by Abba Ibrahim Wada
1 year ago
PDP

Tsohon shugaban majalisar dattawan Nijeriya kuma Wazirin masarautar Ilorin, Dr. Abubakar Bukola Saraki, ya bayyana cewa; bayan ficewar gwamnan jihar Delta daga jam’iyyar PDP zuwa APC, ina ta samun kiran waya daga shugabanni da ƴan jam’iyya matasa da maza da mata, waɗanda suka tsaya tsayin daka wajen ganin an samu ci gaban dimokuraɗiyya.

Yawancin masu kiran waya suna son su ji matsayata a kan fitar gwamnan jihar Delta da ƴan tawagarsa.

  • Wasanni Na Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Ci Gaban Matasa — Gidauniyar Bukola Saraki 
  • Kotu Ta Wanke Tsohon Dogarin Bukola Saraki Kan Zargin Biliyan ₦3.5b

Matsaya ta akan wannan magana shi ne, waɗanda ke son barin PDP su fita tun yanzu, su bar sauran da ke son ci gaba, mu mayar da hankali wajen sake gina jam’iyyar.

ADVERTISEMENT

Yana da muhimmanci duk ɗan Nigeriya ya sani cewa dole ne a tashi tsaye wajen tabbatar da dimokuraɗiyya. Domin tabbatar da hakan, dole ne a samu jam’iyyu masu ƙarfi domin tursasa gwamnati ta yi abin da ya kamata.

Maganar zama jam’iyya ɗaya a ƙasar nan ba abu bane wanda zai zama alheri kasancewar ƙasa ce mai addinai daban-daban da ƙabilu daban-daban da yare daban-daban. Ai abin tsoro ne ma a ce a zauna babu wasu jam’iyyu sai jam’iyya ɗaya, hakan zai nuna cewa mutane ba su da zaɓi, duk abin da aka ga dama shi za a yi musu.

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Saboda haka akwai buƙatar duk wani ɗan ƙasa ya tsaya tsayin daka wajen ganin an samu jam’iyyar adawa mai ƙarfi, wadda za ta karɓi mulki daga hannun jam’iyya mai mulki.

Saƙona ga ƴan jam’iyya shi ne duk wanda yake son ya tafi ga hanya nan, wanda yake son gyara kuma ya zauna a gyara domin mu samu mutane masu amana, waɗanda za mu dinga rufe ƙofa da su kuma ba za su fitar da maganar a waje ba.

Halin da ake ciki yanzu ya bayyana irin matsayar da mutane irina suke kai tun farko na yin shiru domin ganin yadda abubuwa suke tafiya. Tabbas na yadda cewa babu gaskiya a wajen wasu shugabannin daga jam’iyya mai mulki domin yanzu baka san da wa zaka amince kayi maganar sirri ba.

Ya zama dole ƴan jam’iyyar PDP su daina zargin jam’iyya mai mulki da kawo rikici a PDP, domin hakan nuna gazawa ne domin kowa yana yin yadda zai yi ne domin ya samu nasara a zaɓe. Saboda haka ya zama dole a san abin yi, a yi aiki tuƙuru wajen kawo gyara a jam’iyyar PDP.

Tabbas akwai takaici a ce mataimakin ɗan takarar shugaban ƙasa a zaɓen da ya gabata ya fice daga jam’iyya ya koma jam’iyya mai mulki, babu wanda zai gaya maka wani dalilii mai ƙarfi na yin hakan. Kawai hakan yana nuna rashin manufa ne da yadda muka lalace a siyasance.

Tun farko daman shi ne dalilin da yasa nake yawan cewa mu ƙarfafa tsarin mulki da hukumomi a kan ƙarfafa wani mutum guda ɗaya. Duk da fitar gwamnan jihar Delta, har yanzu muna da damar cin zaɓe a ƙasar nan.

Ƴan jam’iyyar mu ya kamata su nutsu, su samu ƙwarin gwiwa domin samun nasara. Mu kalli wannan halin da muke ciki a matsayin wani darasi da zai sa mu sake gina jam’iyyarmu. Akwai nasara a nan gaba

Ina da tabbacin cewa nan ba da jimawa ba shugabancin jam’iyya a matakai daban-daban zai sake zama domin tattauna halin da ake ciki da kawo mafita. Saboda haka babu tashin hankali a cikin abin da ke faruwa.

PDP
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?
  • Abba Ibrahim Wada
    Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji
  • Abba Ibrahim Wada
    Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya
Manyan Labarai

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC
Manyan Labarai

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa
Siyasa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Next Post
Manyan Bankuna 5 Da Suka Samu Ribar Naira Tiriliyan 17.3 A Nijeriya

Manyan Bankuna 5 Da Suka Samu Ribar Naira Tiriliyan 17.3 A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.