Sashin yaki da satar mutane na rundunar ‘yansandan Nijeriya a Wamakko da ke Sakkwato, tare da hadin gwuiwar yan bijilanti a kauyen Laini, sun kama Muhammad Damma Abubakar, mazaunin kauyen Kamasu, cikin karamar hukumar Silame, bisa zargin garkuwa da mutane.
Rundunar ‘Yansandan ta bayyana cewa, an kama Abubakar ne bayan samun sahihan bayanai da suka nuna cewa yana da alaka da wani aikin satar mutane da aka yi a 2024, wanda ya shafi mutane uku – Alhaji Garba Danbaba, Umar Ubandawaki, da Shehu Abubakar, dukkan su mazauna Kamasu.
- An ‘Yi Mummunar Arangama Da ‘Yan Bindiga A Sakkwato
- Gwamnan Sokoto Ya Amince Da Sauya Wa Manyan Sakatarori 25 Ma’aikatu A JiharÂ
Jami’in hulda da Jama’a na rundunar, DSP Ahmad Rufai, ya bayyana cewa, dukkan wadanda aka sace sun gane wanda ake zargin a matsayin daya daga cikin kungiyar da ke da alhakin satar su.
A yayin binciken da aka gudanar, an samu AK-49 da kuma kananan bindigogi 13 daga wajen wanda ake zargin. DSP Rufai ya kara da cewa, ana ci gaba da gudanar da bincike domin gano karin bayanai kan yadda kungiyar ke aiki da kuma yiwuwar wadanda ke cikinta.
Ya kuma tabbatar da cewa, rundunar za ta ci gaba da yaki da aikata laifuka, sannan ya yi kira ga al’umma da su rika kai rahoton duk wani abu da zai iya zama barazana ga tsaro.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp