• English
  • Business News
Tuesday, November 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nunez Ya Jika Wa Liverpool Aiki

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago
Nunez

An bai wa dan wasan gaba na kungiyar kwallon kafa ta Liverpool, Darwin Nunez jan kati, bayan da suka koma zagaye na biyu a lokacin wasa da kungiyar kwallon kafa ta Crystal Palace a wasan da suka tashi 1-1 a filin wasa na Anfield.

Hakan ya sa sabon dan kwallon da Liverpool ta dauka daga kungiyar kwallon kafa ta Benfica a bana, ba zai buga wa kungiyar wasanni guda uku ba a gasar Premier League ta bana wanda kuma babban kalubale ne ga kungiyar.

  • Mohamed Salah Ya Sabunta Kwantiraginsa A Liverpool

Hakan ya biyo bayan jan katin da aka yi masa a wasan farko da ya fara yi a filin wasa na Anfield ranar Litinin din data gabata bayan da dan kwallon tawagar Uruguayan din ya yi wa mai tsaron bayan Palace, Joachim Andersen gware da ka.

Dama dai a makon farko Liverpool ta tashi 2-2 a gidan Fulham, inda Nunez da Mohamed Salah ne suka ci kwallayen kuma kawo yanzu kungiyar ta buga wasanni biyu ba tare da samun nasara ba.

Amma kociyan Liverpool din Jurgen Klopp ya bayyana cewa yana fama da karancin masu cin kwallaye, bayan da Diogo Jota ke jinya, Roberto Firmino bai buga fafatawar da Crystal Palace ba.

LABARAI MASU NASABA

Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 A Ƙauyen Katsina

Nunez wanda ya ci wa Liverpool kwallo daya a wasan Premier League ta bana, ba zai buga haduwa tsakanin Liverpool da Manchester United ba a ranar Litinin a katafaren filin wasa na Old Trafford.

Kawo yanzu ba’a da tabbaci ko Firminho zai warke kafin litinin domin ya buga wa Liverpool wasan mako na uku sannan wasa na gaba da dan kwallon mai shekara 23 da ba zai buga ba shi ne karawa da Bournemouth a ranar Asabar 27 da wanda Liverpool za ta kece raini da Newcastle United.

A dokar gasar filimiyar Ingila dai yin keta da ganganci kan sa a kara hukuncin zuwa wasa hudu, amma ana sa ran dan kwallon wasa uku ne ba zai buga ba kuma hakan babbar matsala ce ga kungiyar mai neman lashe gasar ta firimiya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 
Manyan Labarai

Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika

November 11, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 A Ƙauyen Katsina

November 11, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

November 10, 2025
Next Post
Goro

Goron Jumu'a

LABARAI MASU NASABA

Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 

Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika

November 11, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 A Ƙauyen Katsina

November 11, 2025
An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

November 10, 2025
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

November 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

November 10, 2025
Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

November 10, 2025
Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Masu Zagaye Kusa Da Doron Kasa

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Masu Zagaye Kusa Da Doron Kasa

November 10, 2025
Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

November 10, 2025
Binciken Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Ci Gaba Da Bude Kofa Mai Zurfi A Sin

Binciken Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Ci Gaba Da Bude Kofa Mai Zurfi A Sin

November 10, 2025
Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump

Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump

November 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.