• English
  • Business News
Friday, May 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Zamfara Ta Haɗa Gwiwa Da Oracle A Landan Don Bunƙasa Fasahar Matasa A Jiharta 

by Sulaiman
3 weeks ago
in Labarai
0
Zamfara Ta Haɗa Gwiwa Da Oracle A Landan Don Bunƙasa Fasahar Matasa A Jiharta 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Jihar Zamfara ta rattaba hannu kan wata yarjejeniya da Jami’ar Oracle domin saka hannun jari a harkar inganta rayuwar matasa, inganta ƙarfin ma’aikata, da kuma tattalin arziki na zamani a ƙarƙashin shirin Bunƙasa Fasaha na Jami’ar Oracle (SDI).

 

An sanya hannu kan yarjejeniyar a ranar Talata 29 ga Afrilu, 2025 a Ofisoshin Oracle da ke Landan a Ingila.

  • Ko Kun San Dalilin EFCC Na Kama Gudaji Kazaure
  • Shugaba Xi Ya Isa Moscow Domin Fara Ziyarar Aiki A Rasha

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa, wannan aiki zai samar da haɗin gwiwa tsakanin Hukumar Bunƙasa Fasahar Zamani ta Zamfara (ZITDA) da Oracle.

 

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano

Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

Tawagar jihar Zamfara ƙarƙashin jagorancin Gwamna Dauda Lawal ta haɗa da sakataren gwamnatin jihar, da masu ba da shawara na musamman guda biyu, da babban sakataren ZITDA, tare da Siobhan Wilson, shugaban Oracle na Ingila da kuma babban mataimakin shugaban EMEA.

 

Sanarwar ta ƙara da cewa: “Gwamnatin jihar Zamfara ta rattaba hannu kan wata yarjejeniya mai muhimmanci tare da Oracle don bunƙasa fasahar dijital a faɗin jihar, wanda aka samu ta hanyar Hukumar Bunƙasa Fasahar Sadarwa ta Zamfara (ZITDA), haɗin gwiwar za ta yi amfani da ƙwarewa da ayyukan koyo na makarantar Oracle da jami’ar Oracle a ƙoƙarinsu na kawo sauyi.

Zamfara

“Haɗin gwiwar yana nuna sadaukar da kai ga ilimi da saka hannun jari a makomar matasan Zamfara, ma’aikata, da tattalin arzikin dijital.

 

“Makarantar Oracle, shirin ilimi na taimakon jama’a na duniya yana koyar da ilimin fasaha, gami da manhaja da samun damar sanin ilimin fasahar software na kwamfuta ga malamai da ɗalibai a duk duniya.

 

“Tare da tallafin Hukumar Bunƙasa Fasahar Sadarwa ta Zamfara (ZITDA), za a samar da waɗannan albarkatun ga ingantattun manyan makarantu a faɗin Zamfara.”

 

“ZITDA za ta taimaka wajen jagorantar ayyukan makarantar Oracle Academy a cikin babbar manhajar karatu ta Zamfara, tana ba wa malamai kayan aiki da albarkatun da suke buƙata don koyar da ɗalibai dabarun fasaha da kuma samun takardun ƙwarewa na Oracle.

 

“Bugu da ƙari, Shirin Jami’ar Oracle (SDI), shiri ne na duniya wanda ke koyar da abubuwa na musamman a duniya ba tare da kashe ko kobo ba ga ɗaliban da suka cancanta, kuma zai ƙara faɗaɗa damarmaki ga ɗalibai a Zamfara.

 

“Ta hanyar haɗin gwiwar Learning Portal tare da ZITDA, Jami’ar Oracle na shirin ba da damar samun hanyoyin ilmantarwa kyauta da takardun shaida ga mahalartan da suka cancanta a faɗin Zamfara. Wannan ya haɗa da tafiye-tafiye na ilmantarwa wanda ke ba da horo na ƙwarewa na sama da sa’o’i 200 a fannonin da ake buƙata kamar Cloud, Ƙirƙirarriyar Basira ta AI, Data Science da APEX.”

Zamfara

A jawabinsa a wajen rattaba hannu kan muhimmiyar yarjejeniyar, Gwamna Dauda Lawal ya jaddada cewa haɗin gwiwa da Oracle na daga cikin ƙudirin gwamnatinsa na mayar da jihar Zamfara wata cibiya ta ƙirƙire-ƙirƙire, ilimi, da fasahar zamani.

 

Ya ce, “A madadin gwamnati da na al’ummar jihar Zamfara, ina miƙa godiya ta ga Oracle bisa yadda ta yi imani da manufofinmu da kuma haɗin kai da mu kan wannan tafiya ta kawo sauyi.”

 

“Abin da muke yi a yau ya wuce fasaha, samar wa al’umma madogara ne, samar da hanyoyi, da kuma buɗe damarmakin da ke gaba. Ta hanyar saka hannun jari a ilimin dijital, muna ba neman ƙore talauci, rashin aikin yi, da kuma hana yanke ƙauna.”

 

“Ina godiya ga Oracle don tsayawa tare da mu – yarda da ƙarfin haɗin gwiwa da sanin manufar mu. A yau, ba kawai muna sanya hannu kan takarda ba ne; amma muna yin alƙawari: “Alƙawarin cewa kowane yaro a Zamfara zai samu dama mai kyau don ƙaddanar da burin sa na rayuwa, koyo, da kuma samun nasara. Alƙawarin cewa fasaha za ta zama gadar mu ta zuwa ta samun tattalin arziki mai ƙarfi. Kuma alƙawarin cewa Zamfara ba za ta shiga cikin juyin juya halin dijital kawai ba – a’a mu za mu jagoranci shi.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ko Kun San Dalilin EFCC Na Kama Gudaji Kazaure

Next Post

Almundahana: LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar

Related

Yadda Rikici Ya Yi Sanadin Kashe DPO A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano

10 hours ago
Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja
Labarai

Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

12 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

12 hours ago
Atiku Ya Caccaki Gwamnatin Tinubu, Ya Yi Gargaɗi Kan Cin Sabon Bashi
Manyan Labarai

Atiku Ya Caccaki Gwamnatin Tinubu, Ya Yi Gargaɗi Kan Cin Sabon Bashi

16 hours ago
Zaman lafiya
Labarai

MDD Ta Gudanar Da Bikin Ranar Tunawa Da Dakarun Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Duniya Ta 2025

18 hours ago
Buhari Ya Yabi Tinubu, Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Rage Tsammani Da Dogon Buri
Manyan Labarai

Buhari Ya Yabi Tinubu, Ya Bukaci ‘Yan Nijeriya Su Rage Tsammani Da Dogon Buri

19 hours ago
Next Post
Almundahana: LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar

Almundahana: LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam'iyyar

LABARAI MASU NASABA

Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo

Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo

May 29, 2025
An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 

An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 

May 29, 2025
Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600

Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600

May 29, 2025
Yadda Rikici Ya Yi Sanadin Kashe DPO A Kano

‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano

May 29, 2025
Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda

Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda

May 29, 2025
Sin Ta Cimma Nasasar Harbar Na’urar Nazarin Tauraro a Sararin Sama Mai Lakabin “Tianwen-2”

Sin Ta Cimma Nasasar Harbar Na’urar Nazarin Tauraro a Sararin Sama Mai Lakabin “Tianwen-2”

May 29, 2025
Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

Ana Fargabar Mutane Da Dama Sun Rasu Sakamakon Ambaliyar Ruwa A Neja

May 29, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa

May 29, 2025
AU Ta Jinjinawa Goyon Bayan Sin Ga Ci Gaban Nahiyar Afrika

AU Ta Jinjinawa Goyon Bayan Sin Ga Ci Gaban Nahiyar Afrika

May 29, 2025
Sin Da Kasashen Yankin Pasifik Sun Yi Nasarar Gudanar Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Karo Na Uku

Sin Da Kasashen Yankin Pasifik Sun Yi Nasarar Gudanar Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Karo Na Uku

May 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.