ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

MDD Ta Gudanar Da Bikin Ranar Tunawa Da Dakarun Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Duniya Ta 2025

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Zaman lafiya

A ranar Laraba ne aka gudanar da bikin Tunawa da Ranar Dakarun Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Duniya a ofishin Majalisar Dinkin Duniya (MDD) na Nijeriya. Babban bako a taron, Babban Hafsan Hafsoshin Tsaron Nijeriya Janar Christoper OFR. Inda a jawabinsa bayan maraba da baki ya ce, “Tunawa da Ranar Dakarun Wanzar Da Zaman Lafiya Ta MDD Ta 2025, taro ne na tunatar da sadaukarwar da jarumanmu maza da mata suka yi wajen sadaukar da rayuwarsu don tabbatar da zaman lafiya da tsaro a duniya.”

Ana aikin ne domin babu wata al’umma da za ta iya jure fuskantar tashe-tashen hankula a duniya, rikicin jin kai da karuwar rashin tsaro. Don haka dole ne mu ci gaba da yin aiki tare da yin magana da murya daya don samar da zaman lafiya, adalci da mutunci ga kowa. Dangane da haka, Rundunar Sojin Nijeriya ta ci gaba da dagewa wajen bin ka’idojin Yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya.

  • Hadin Gwiwar Sin Da Yankin Turai Na Kara Kawo Haske Ga Tattalin Arzikin Duniya
  • Yadda Rashin Ɗaukar Wani Maniyyaci Ya Hana Jirgi Tafiya Har Sai Da Ya Dawo Ya Ɗauke Shi

Yana da kyau a lura cewa a matsayinta na mamba a Majalisar Dinkin Duniya, Nijeriya tun bayan samun ‘yancin ke ta ci gaba da tsayawa tsayin daka wajen bayar da gudummawarta wajen wanzar da zaman lafiya da magance rikice-rikice a duniya. Bisa ga haka, sojojinmu sun yi aiki a karkashin tutar Majalisar Dinkin Duniya tare da girmamawa da ban mamaki a yankuna da dama na warware rikici a duniya.

ADVERTISEMENT

Hakika, Nijeriya na daya daga cikin kasashen Afirka da ke kan gaba wajen bayar da gudunmowa ga ayyukan wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya kuma jigo a kwamitin wanzar da zaman lafiya.

Wannan ba wai yana nuna karfin sojojinmu na fuskantar barazanar da ke tasowa bane kawai, har ma da nuna imaninmu cewa zaman lafiya a duniya nauyi ne na dukkan kasashe da masu ruwa da tsaki.”

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

Shima a nasa jawabin Janar Martin Luther Agwai cewa ya yi, “Aikin wanzar da zaman lafiya na daya daga cikin muhimman aikin Majalisar Dinkin Duniya da ake iya gani, inda sama da sojoji 87,000 ke sanye da rigar wanzar da zaman lafiya da farar hula suka taka rawa a cikin wasu ayyuka 12, daga Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo zuwa Lebanon, daga Sudan zuwa Mali. Nijeriya kuma na wakiltar ayyuka guda 8.”

Wadannan jajirtattun maza da mata suna taimakawa wajen daidaita yankuna, ba wa fararen hula kariya, tallafawa tsagaita wuta, da sake gina da amana inda ta lalace.

Mahimmanci lamari shi ne, tun lokacin da aka kafa tawagar wanzar da zaman lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya ta farko a shekara ta 1948, dakarun wanzar da zaman lafiya sun ceto mutum sama da miliyan biyu daga kasashe sama da 125 cikin ayyuka 71 da suka gudanar.

Tun da fari a jawabinsa na maraba, Jami’in Majalisar Dinkin Duniya Kuma Mai Kula Da Ayyukan Jin Kai a Nijeriya Mohammed Malick Fall, maraba da zuwan bikin cika shekaru 77 na ayyukan samar da zaman lafiya na MDD ya yi, inda ya ce “Taro ne mai muhimmanci kuma ya zo daidai da cika shekaru 80 da kafuwar Majalisar Dinkin Duniya,” in ji shi.

“A tsawon tarihinta, Majalisar Dinkin Duniya babban aikinta ga al’ummar duniya shi ne inganta zaman lafiya, tsaro, ci gaba, da mutunta bil’adama, kuma ta yi fice a wajen cimma wadannan manufofi.”

“Tun daga 1948, Majalisar Dinkin Duniya ta sa ido kan ayyukan wanzar da zaman lafiya fiye da 70, da ceton rayuka da dama da kuma yin aiki a matsayin mai magance manyan tashe-tashen hankula.

A halin yanzu, sama da dakaru 87,000 masu sanye da kaki ana tura su cikin ayyuka mabanbanta kamar 12 a duniya.

Wanzar da zaman lafiya ya kasance daya daga cikin abubuwan da Majalisar Dinkin Duniya ta fi gani da inganci.”

“Karni na 21 ya zo da qalubalen tsaro da ba a tava ganin irinsa ba kuma masu alaqa da juna. Wadannan suna bukatar sabbin hanyoyi, kakkarfan hadin gwiwa na yanki da na duniya, da kuma sake nazarin yadda muke gudanar da ayyukan zaman lafiya-musamman yayin da rarrabuwar kawuna na siyasa ke kara hana shawo kan lamarin.

Wannan shi ne dalilin da ya sa muka sanya wa taron ranar dakarun wanzar da zaman lafiya ta Majalisar Dinkin Duniya a yau, taken “Makomar wanzar da zaman lafiya,” kuma ya dace sosai, in ji shi.

MDD
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
Ɗalibai Sun Rubuta Jarrabawar WAEC Cikin Dare A Duhu

Ɗalibai Sun Rubuta Jarrabawar WAEC Cikin Dare A Duhu

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.