• English
  • Business News
Wednesday, May 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

by Yusuf Shuaibu
3 days ago
in Labarai
0
Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Manajan Darakta na kamfanin bunkasa ma’adanai a Kaduna, Injiniya Shuaibu Kabir Bello, ya sanar da cewa a kwanan nan ne kamfanin ya gano albarkatun ma’adanai daban-daban har 73 a duk fadin jihar, wanda wannan gagarimin ci gaba ne da ke shirin canza yanayin tattalin arzikin Kaduna.

“Da wannan arzikin ma’adanai, za mu samar da dubban guraben ayyukan yi ga matasa a fadin Jihar Kaduna. Wannan damar za ta samar da ci gaba tare da fata da wadata ga matasanmu, “in ji shi.

  • EFCC Ta Kama Matashi A Kaduna Bisa Zargin Wulaƙanta Naira A Bidiyon Barkwanci
  • Za Mu Magance Matsalar Ruwan Sha Kafin Ƙarshen 2025 A Kaduna – Uba Sani

Bello ya bayyana hakan ne yayin da yake zantawa da manema labarai a hedikwatar kamfanin da ke Kaduna. Ya bayyana cewa kamfanin a shirye yake don daukar matakai masu tsauri wajen jawo hankalin masu saka hannun jari da habaka bangaren hakar ma’adanai.

Ya bayyana cewa Jihar Kaduna tana da albarkatun ma’adanai iri-iri, ciki har da zinariya, tagulla, azurfa, bakin karfe da sauransu.

Da yake jaddada muhimmancinsu, Bello ya ce, “Muna da komai daga zinariya, tin, tagulla, azurfa, bakin karfe, bakin dutse, Lithium da dai sauransu, Lithium wani muhimmin bangare ne na canjin makamashi na duniya.”

Labarai Masu Nasaba

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Ya kara da cewa bukatar kasa da kasa game da karfin ma’adinai na Kaduna yana karuwa, tare da masu saka hannun jari da yawa wadanda suke bincike kan yadda za su yi amfani da wadannan albarkatun da ba a taba amfani da su ba.

“Baya ga wannan, muna da ma’adanan karfe. Kamfanin ‘African Mines’ ya riga ya zo Kaduna don hakar wannan albarkatun, wanda ya nuna a fili cewa Kaduna tana da ma’adanan karfe da za a iya gudanar da kasuwancinsu,” in ji shi.

Bello ya jaddada cewa tsarin kamfanin yana nuna jajircewa don kokarin killace iyakokin ma’adinai da kuma habaka su.

Ya ce tun lokacin da aka kafa kamfanin, hukumar gudanarwaar kamfanin ta ba da fifiko ga ayyukan da ke sanya alhakin muhalli da zamantakewar al’umma a gaba a ayyukanta.

Haka kuma manajan daraktan ya kuma yaba wa Gwamna Uba Sani saboda goyon bayan da yake bayarwa ga bangaren hakar ma’adanai, yana mai cewa a karkashin jagorancin gwamnan, kamfanin ba wai kawai a shirye yake ba har ma yana da cikakkiyar kayan aiki don samar da sakamako mai kyau.

“Ana sa ran wannan kokari zai samar da ci gaba a hakar ma’adanai tare da bude hanyoyin arziki a bangaren ma’adanai, samar da dubban ayyuka, da kuma habaka ci gaban tattalin arziki ba kawai a Kaduna ba har ma a duk fadin Nijeriya,” in ji shi.

Ya kuma tabbatar wa masu saka hannun jari na cikin gida da na waje samar da yanayi mai aminci wanda ke karfafa kirkire-kirkire da ci gaba na dogon lokaci.

Bello ya kuma sanar da cewa kamfanin bunkasa ma’adanai na Kaduna a shirye yake ya yi maraba da masu saka hannun jari da ke da sha’awar yin amfani da albarkatun kasa na jihar.

Ya bayyana tashar sarrafa lithium ta Kangimi, wacce ke aiki a karfin tan 5,000 a kowace rana, a matsayin babban ci gaba a tafiyar hakar ma’adinai ta jihar.

“Bisa jajircewar kamfanin wajen samar da aminci da ci gaba mai dorewa, Kaduna za ta kasance a matsayin babban wurin saka hannun jari,” in ji shi.

Ya nuna godiya ga Gwamna Uba Sani, yana mai cewa, “Godiya ga kokarin da Gwamna Uba Sani ya yi, muna shaida canji mai ban mamaki a bangaren hakar ma’adanai wanda ke bude hanya don kyakkyawar makoma mai kyau.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KadunaMa’adanai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

Next Post

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Related

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 
Labarai

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

7 hours ago
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe
Labarai

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

8 hours ago
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

10 hours ago
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya
Labarai

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

11 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

13 hours ago
Wata Mata Ta Kashe Dan Hayar Da Ke Gidanta A Ondo
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m

16 hours ago
Next Post
Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

LABARAI MASU NASABA

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

Binciken Jin Ra’ayoyi Na CGTN: Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Ce Harajin Fentanyl Ya Gurgunta Hadin Gwiwar Amurka Da Sin Kuma Fiye Da Kashi 90% Na Jama’a Sun Koka Da “Jarabar” Amurka Ta Cin Zarafi

May 13, 2025
Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

Tsaro: Gwamna Lawal Ya Raba Motoci 140 Ga Jami’an Tsaro A Zamfara 

May 13, 2025
Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

Sin Tana Kara Kwatar Wa Kasashe Masu Tasowa ’Yanci

May 13, 2025
Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

Masarautar Saudiyya Ta Raba Magunguna Kyauta Ga Masu Matsalar Ido A Jihar Yobe

May 13, 2025
Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

Hadin Kai Da Cin Moriya Tare Ne Hanya Mafi Dacewa Wajen Daidaita Matsalar Dake Tsakanin Sin Da Amurka

May 13, 2025
Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe

May 13, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Tattauna Da Takwaransa Na Kasar Brazil

May 13, 2025
Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

Majalisa Ta Yi Watsi Da Ƙudirin Dokar Karɓa-karɓa A Kujerar Shugaban Ƙasa A Tsakanin Shiyyoyin Nijeriya

May 13, 2025
An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

An Nuna Fasahar Waken Pingtan Na Kasar Sin A Najeriya

May 13, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

May 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.