ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tarihin Sarkin Katsina Muhammadu Dikko (5)

by Idris Aliyu Daudawa
1 year ago
Katsina

Sarkin Katsina Muhammadu Dikko ya gina Asibiti da makarantar Boko wadda ita ce ta farko a tarihin ilimi a Arewacin Nijeriya a shekarar 1922 da ake kira da suna Katsina College(Kwalej).Har ila yau Sarkin Katsina Muhammadu Dikko ya  daukaka ilimin Boko saboda ai ya tura ‘ya’yansa da sauran wasu su yi karatun Boko,wanda a lokacin ake  matukar kyama,a karkashin Turawan mulkin mallaka na kasar Ingila.

A shekarar 1935, Sarkin Katsina Muhammadu  Dikko ya rushe Masallacin da Usman Dallaje ya gina lokacin mulkin Dallazawa wanda Umarun Dallaje ya gina, ana kiran Masallacin da sunan Masallacin Dutsi.Shi ne kuma Sarkin Katsina na farko ya tafi aikin Hajji cikin mota a shekarar 1921,daga can kuma shi ne Sarki na farko wanda ya fara tafiya zuwa Ingila,inda shi da ‘yan tawagarsa suka gana da  King George V, ya kuma kai ziyara zuwa shahararren gidan namun dajin nan da ake kira da suna London Zoo ko gidan namun daji,ya sake komawa Ingila a shekarun 1924 da kuma 1937.

  • ‘Yansanda Sun Daƙile Yunƙurin Yin Garkuwa Da Mutane A Katsina
  • Radda Ya Raba Wa Manoma Taki A Jihar Katsin

Bayan da kasar Birtaniya ta mamaye Katsina,Katsina  ba tada wata matsalar yaki da kowa.Muhammadu Dikko wanda shi ya iya hawan Doki sai ya bada karfi a rika amfani da Dawakin da ake amfani da su wajen yaki,a rika yin wasa da su kamar Polo .Dikko ya gina babban filin wasa na Polo wanda har yanzu ana amfani da shi a Katsina.Sarkin Katsina Muhammadu Dikko ya ba, ‘ya’yansa da sauran wasu mutane kwarin gwiwa na su yi wasan na Polo .Wanda ya gaji Sarkin Katsina Muhammadu Dikko mai suna Usman Nagogo,ya kai  ga nasarar samun kwarewa a wasan na Polo wanda wani dan wasan Polo daga Afirka ya taba samu/kaiwa.Marigayi Sarkin Katsina Usman Nagogo shi ne Shugaban kungiyar masu wasan kwallon Polo na Nijeriya.

ADVERTISEMENT

 

Rasuwa da wanda ya gaje shi

LABARAI MASU NASABA

Farashin Mai Na Iya Sauka Har Zuwa Dala $60 Kan Kowanne Ganga

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

Sarkin Katsina Muhammadu Dikko Allah ya yi ma shi rasuwa,a shekarar 1944 da ba’a dade da shigarta ba,bayan ya sanu damuwa daga rashin lafiya, wannan shi yasa aka fara fafutukar neman wanda zai gaje shi.Ta bnagare daya akwai gidan Sarautar Dallazawa  a karkashin jagorancin Yarima, wanda shi dan Sarkin Katsina Abubakar ne wanda yake ganin Sarautar Katsina wata dama ce ta shi,sai ta daya bangaren kuma akwai ‘ya’yan marigayi Sarkin Katsina Muhammadu Dikko,wadanda su ma suna da matukar karfi,wadanda daga cikinsu ma da akwai wata ‘yar jayayya kan wanda zai gaji mahaifin nasu. Watan Maris 1944,sai masu zaben Sarki suka zabi  karami daga cikin ‘ya’yan Dikko da ake kira da suna Usman Nagogo,wanda shi ne Turawan mulkin mallaka na Ingila suke so saboda yana da ilimin Boko,da kuma yadda ya kasance kusa da mahaifinsa.An nadawa Usman Nagogo rawanin Sarautar ranar  19 Mayu 1944 Yayin da shi kuma marigayi Sarkin Katsina Muhammadu Dikko aka rufe shi,a Lambun da ke fadar Sarkin Katsina Dikko

Katsina
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

MASU ALAKA

Farashin Mai Na Iya Sauka Har Zuwa Dala $60 Kan Kowanne Ganga
Labarai

Farashin Mai Na Iya Sauka Har Zuwa Dala $60 Kan Kowanne Ganga

June 20, 2026
Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina
Labarai

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

June 20, 2026
Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
Labarai

Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

June 20, 2026
Next Post
Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne

LABARAI MASU NASABA

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace

June 20, 2026
Farashin Mai Na Iya Sauka Har Zuwa Dala $60 Kan Kowanne Ganga

Farashin Mai Na Iya Sauka Har Zuwa Dala $60 Kan Kowanne Ganga

June 20, 2026
Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu

June 20, 2026
Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

June 20, 2026
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

June 20, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

June 20, 2026
Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.