• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wang Yi: Ziyarar Shugaba Xi A Rasha Ta Kara Yaukaka Kawance Da Daidaito Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

by CGTN Hausa and Sulaiman
6 months ago
Wang Yi

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya ce ziyarar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gudanar a Rasha ta kara yaukaka cikakkiyar huldar abokantaka ta hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare a sabon zamani tsakanin sassan biyu, kuma ta yi tasiri wajen hade tafiyar sassan kasa da kasa a fannin wanzar da oda tsakanin kasashen duniya bayan aukuwar yaki, da ingiza tasirin sassa daban daban a harkokin duniya, da sake gina kyakkyawan tsarin siyasar duniya.

Wang Yi, wanda ya bayyana hakan yayin taron manema labarai na jiya Asabar, ya ce bisa gayyatar da shugaban kasar Rasha Vladimir Putin ya yi masa, shugaba Xi ya gudanar da ziyarar aiki a Rasha, tare da halartar bikin cika shekaru 80 da cimma nasarar babban yakin kare kasa na tsohuwar tarayyar Soviet tsakanin ranakun Laraba zuwa Asabar.

  • Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa
  • 2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

Yayin ziyarar, shugaba Xi tare da takwaransa na Rasha sun gudanar da zuzzurfar tattaunawa game da batutuwan da suke jan hankalinsu a tsawon kusan sa’o’i 10, kuma sakamako game da batun siyasa mafi jan hankali da aka cimma sanadiyyar ziyarar, shi ne sanya hannu da shugabannin biyu suka yi kan takardar hadin gwiwa, don zurfafa cikakkiyar huldar abokantaka ta hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare a sabon zamani tsakanin sassan biyu.

Ministan harkokin wajen kasar Sin ya kara da cewa, halartar bikin nasarar da tsohuwar tarayyar Soviet ta samu a ranar Jumma’a 9 ga watan nan da shugaba Xi ya yi, ya sake tabbatar da aniyar kasar Sin ta yin aiki tare da sauran kasashe, wajen tabbatar da hakikanin abubuwan da suka faru yayin yakin duniya na 2, da burin hadin kai don kare odar kasa da kasa bayan yaki.

Kazalika yayin ziyarar, shugaba Xi ya kuma yi cudanya da jagororin siyasa daga kasashe daban daban, wadanda suka halarci bukukuwan da suka gudana, tare da gudanar da taruka da manyan shugabannin duniya daga nahiyoyi 3, inda suka cimma matsaya mai ma’ana dangane da goyon bayan juna, da kare salon cudanyar mabambantan sassa, da nuna adawa da siyasar nuna karfin tuwo da cin zali. (Saminu Alhassan)

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

November 5, 2025
Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

November 5, 2025
CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika
Daga Birnin Sin

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025
Next Post
Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025
Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

November 5, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 5, 2025
Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

November 5, 2025
Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.