• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027

by Sadiq
3 months ago
in Siyasa, Manyan Labarai
0
Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa Takara A 2027
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Babban Birnin Tarayya, Abuja, Nyesom Wike, ya gargaɗi jam’iyyar PDP da ka da ta kuskura ta miƙa tikitin takarar shugaban ƙasa ga wani ɗan Arewa a zaɓen shekarar 2027.

Wike ya faɗi haka ne a lokacin wata ganawa da ya yi da manema labarai a ranar Litinin, inda ya bayyana cewa jam’iyyar na yi wa tsarin adalci da daidaito barazana idan har ta sake yin kuskuren da ta yi a 2023.

  • Yanzu-yanzu: Matatar Ɗangote Ta Sake Karya Farashin Man Fetur
  • Kaico: Wani Ƙani Ya Kashe Saurayin Yayarsa A Kano

“Me zai hana PDP ta ce tun da gaskiya ake nema, ɗan takarar shugaban ƙasa na 2027 zai fito daga kudu? Amma sun fi son sake yin wayo irin na bara, wanda ya sa jam’iyyar ta fuskanci rikici kuma ta sha kaye,” in ji Wike.

Wike ya ce yana da muhimmanci jam’iyyar ta bayyana matsayinta a fili tun kafin lokaci ya ƙure, domin hakan zai taimaka wajen sake gina amincewa da haɗin kai a tsakanin mambobin jam’iyyar.

Ya ƙara da cewa, “Idan shugaban ƙasa daga Kudu ya samu nasara a 2027, to a 2031 zai zama dama ce ga Arewa.

Labarai Masu Nasaba

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

“Amma idan yanzu aka sake bai wa Arewa takara, wannan tsari tsakanin Arewa da Kudu zai ruguje.”

Wike, wanda tsohon gwamnan Jihar Ribas ne, yana daga cikin fitattun jiga-jigan PDP da ke goyon bayan daidaito da karɓa-karɓar mulki tsakanin Arewa da Kudu domin tabbatar da zaman lafiya da haɗin kan ƙasa.

A baya dai, rikici wajen tantance daga inda ɗan takarar PDP zai fito ya janyo rabuwar kai a cikin jam’iyyar, lamarin da ya taimaka wajen rage ƙarfinta a zaɓen 2023.

Masana siyasa na ganin wannan gargaɗi na Wike na iya sake haifar da muhawara a jam’iyyar, musamman yayin da ta ke shirin fuskantar babban zaɓen 2027.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GargaɗiPDPSiyasaWike
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Ta Biya Dukkanin Bashin IMF Na COVID-19

Next Post

Bam Ya Hallaka Ma’aikatan Hukumar Ilimi 2 A Hanyar Damboa-Maiduguri

Related

Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

3 hours ago
Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 
Siyasa

Gwamna Dauda Zai Karɓi Baƙuncin Gwamnonin PDP A Zamfara 

6 hours ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

10 hours ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

13 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

14 hours ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

22 hours ago
Next Post
Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno

Bam Ya Hallaka Ma’aikatan Hukumar Ilimi 2 A Hanyar Damboa-Maiduguri

LABARAI MASU NASABA

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

August 22, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

August 22, 2025
Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

August 22, 2025
Jihar Xizang Ta Baiwa Duniya Mamaki Da “Canji Mai Girma” Da Ta Samu a Cikin Shekaru 60 Da Suka Gabata 

Jihar Xizang Ta Baiwa Duniya Mamaki Da “Canji Mai Girma” Da Ta Samu a Cikin Shekaru 60 Da Suka Gabata 

August 22, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Kayan Maye Na Miliyan 680 A Katsina

Hukumar Kwastam Ta Kama Kayan Maye Na Miliyan 680 A Katsina

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.