Kungiyar Malaman jami’o’i ta kasa (ASUU) reshen Jami’ar Nsukka (UNN) ta yi barazanar maka hukumar shirya jarabawar shiga makarantun gaba da sakandire ta Kasa (JAMB) a gaban kotu saboda mummunar faduwar da Dalibai suka yi a a jarabawar shiga jami’a (UTME) ta shekarar 2025.
Shugaban kungiyar ASUU-UNN, Kwamared Óyibo Eze ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a garin Nsukka na jihar Enugu a ranar Laraba.
- Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
- Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Oyibo ya ce, shiyyar da tafi samun mummunan sakamakon jarabawar itace Kudu-maso-Gabas. Lallai wannan zagon kasa ne da JAMB ta shirya da gangan na hana yaran shiyyar shiga manyan makarantu.
“Ofishina ya cika da tarin jama’a suna ta kiraye-kiraye kan wannan mummunan sakamakon da aka samu a jarabawar JAMB ta 2025.
“ASUU za ta kalubalanci wannan sakamakon a gaban babbar kotu idan JAMB ta gaza sake duba sakamakon da kuma bai wa dalibai makin da suka cancanta.” In ji shi
Ya yi kira ga gwamnonin jihohin Kudu-maso-Gabas da su tashi su kalubalanci abin da ya kira da rashin adalci domin hana dalibai daga shiyyar samun shiga manyan makarantu a kasar nan.
LEADERSHIP ta ruwaito cewa, shugaban JAMB, Farfesa Ishaq Oloyede, a ranar Laraba ya bayyana shirin sake gudanar da jarabawar ga dalibai da suka fito daga jihohin Kudu maso Gabas da Legas.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp