ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ƙungiyar Fulani Makiyaya Ta Nuna Damuwarta Na Ɓacewar Mataimakin Shugabanta

by Shehu Yahaya
7 months ago
Fulani

Ƙungiyar Fulani Makiyaya ta kasa (MACBAN) ta nuna nuna damuwarta dangane rashin sanin halin da mataimakin shugaban kungiyar na kasa, Injiniya Mannir Atiku Lamido, tsawon shekaru biyu babu labarinsa.

A wani taron manema labarai a Kaduna, wanda sakataren kungiyar Alhaji Bello Aliyu Gotomo, ya yi ya bayyana rashin gamsuwarsu da irin matakin da jami’an tsaro suke dauka wajen gano halin da mataimakin shugaban nasu yake ciki duk da cewa suna ikirarin yin bakin kokarinsu.

  • Lokaci Ya Yi Da Za A Kawo Karshen Musguna Wa Fulani – Dakta Awwal 
  • Kungiyar Fulani Ta MACBAN Ta Nesanta Kanta Daga Zanga-zangar Matasa

Haka zalika, ya bayyana danuwarsu dangane da yadda matsalar rashin tsaro take kara ta’azzara a jihohin Arewacin kasar nan, musamman jihohin Adamawa da Borno da Nija da Katsina da dai sauransu, inda ya ce akwai bukatar hukumomin tsaro su kara zage damtse wajen kawo saukin lamarin.

ADVERTISEMENT

Ya ci gaba da cewa, “Jami’an tsaro sun shaida mana cewa suna bakin kokarinsu wajen gano halin da Injiya Manir Atiku yake ciki, amma abin da ya ba mu tsoro da shakku shi ne, sun ce sun yi kokarin bibiyar lambar wayarsa domin gano inda yake amma abin da bai yiwuba saboda a cewarsu, an goge komai a wayarsa wanda babu wata hanya da za a iya gano inda yake ta hanyar bibiyar wayarsa. Sun ce a yanzu babu wani bayani da za a iya samu dangane da batar nasa.

“Muna kira ga gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro da su taimaka mana su gano halin da dan uwanmu yake ciki, yau shekaru biyu kenan babu labarinsa.”

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Ceton Dukkan Ɗalibai 230 Da Aka Sace A Neja

Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

Mataimakin shugaban kungiyar MACBAN ta kasa ya bace ne a ranar 20 ga watan Yuni na shekarar 2023 a garin Zariya, inda aka tsinci motarsa a bakin hanya a bude, lamarin da haifar da fargaba da jimami, wanda har yanzu babu wani bayani dangane da halin da yake ciki.

Sai dai sakataran ya bayyana jin dadinsu bisa samar da ma’aikatar bunkasa harkokin Fulani da Shugaban kasa Bola Tinubu ya yi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Ceton Dukkan Ɗalibai 230 Da Aka Sace A Neja
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Ceton Dukkan Ɗalibai 230 Da Aka Sace A Neja

December 22, 2025
Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

December 22, 2025
An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Next Post
Dalilin Ƴansandan Kano Na Tsare Wasu Awaki

Dalilin Ƴansandan Kano Na Tsare Wasu Awaki

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Ceton Dukkan Ɗalibai 230 Da Aka Sace A Neja

Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Ceton Dukkan Ɗalibai 230 Da Aka Sace A Neja

December 22, 2025
Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

December 22, 2025
An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.