• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Tabarbarewar Tsaro Ta Kara Yawan Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta

by Rabi'u Ali Indabawa
3 months ago
in Manyan Labarai
0
Yadda Tabarbarewar Tsaro Ta Kara Yawan Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Masu ruwa da tsaki na ci gaba da nuna damuwarsu kan yara sama da miliyan 10 da ba sa zuwa makaranta a Nijeriya, inda akasarinsu ke zaune a yankin arewacin kasar.

Da yawa daga cikin wadannan yara kamar yadda bayanan LEADERSHIP suka gano, an ce an tilasta wa wadannan yara barin makaranta ne saboda tashe-tashen hankula da wasu nau’ika na rashin tsaro.

  • Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 
  • Ƙungiyar ’yan Majalisar Dokokin Ƙasa Ta APC Ta Amince Da Takarar Tinubu A Zaɓen 2027 

‘Yan Nijeriya da dama da abin ya shafa sun ce kasar na fuskantar bala’in rashin ilimi mai cike da ban tsoro, ganin yadda aka tilasta wa miliyoyin yara barin ajujuwa ba da son ransu ba, ta hanyar ayyuka na ta’addanci, rikice-rikice, da sauran nau’ukan tashe-tashen hankula musamman a yankin Arewa.

Misali, bisa binciken da aka yi, tsakanin shekarar 2012 zuwa 2016 kadai, an kashe malamai sama da 600 a lokacin da suke gudanar da aiki domin gina kasa.

Bayanai daga LEADERSHIP sun gano cewa yawancin yaran suna tsakanin shekaru biyar ne zuwa 14, kuma sama da kashi 60 cikin 100 na wadannan yara suna zaune ne a yankin Arewa maso Gabas, yankin da ke fama da tashe-tashen hankula da rashin matsugunai, da kuma tsananin talauci.

Labarai Masu Nasaba

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Bincike ya yi nuni da cewa an bar dukkan al’ummomi ba tare da ingantattun makarantu ba a jihohi kamar Borno, Yobe, da Adamawa.

Sama da makarantu 1,500 ne aka lalata tun farkon rikicin Boko Haram, inda sama da malamai 19,000 suka rasa matsugunansu, kuma da yawa ma suna fargabar komawa.

‘Yan mata suna cikin hadari, galibi ana tilasta musu auren wuri ko aikin gida ko aikin jima’i maimakon a ba su damar koyo.

Wata kwararriyaa fannin ilimi da ke zaune a Jos, Jihar Filato, Misis Peace Pernam, ta ce, “Ilimi wata hanya ce ta rayuwa mai muhimmanci da ke kawar da fatara, rage matsalar tsaro, da samar da ci gaban kasa, duk da haka, ga miliyoyin yara a yankin Arewa maso Gabas, cikin matsanancin rikici, rashin kyakkyawan shugabanci, wadanda rashin sanya hannun jari ke yanke jin dadin rayuwarsu.

Al’amarin wadannan yaran bai tsaya kadai kididdiga ba. Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) ya tabbatar da abin da ba a yi tsammani ba: Nijeriya ce ta fi kowacce kasa yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a duniya. Idan ka tara uku za ka samu daya daga cikinsu ba ya zuwa makaranta, wato ba ya samun ilimin boko a halin yanzu.

“Wannan matsalar ba ta tsaya kadai ga ilimi ba, al’amari ne dake bukatar taimakon gaggawaa kasa.

Idan ba a dauki matakin gaggawa ba, Nijeriya na fuskantar afkawa hadarin kasa yin kafada da sa’anninta, wajen ci gaba sace jama’a da rashin kyakkyawar gami da kakaba wa jama’a talauci, tsatsauran ra’ayi, da rashin zaman lafiya.”

A cewar wani mai sharhi kan al’amuran jama’a, Ahmed Idris, matsalar ilimi a Nijeriya na kara ta’azzara, musamman a yankunan da ke da karancin makarantu.

Ya ce yara da yawa har yanzu suna tafiya mai nisa zuwa makaranta, idan kuma sun halarci makarantar za ka samu babu kwararrun malamai.

Wani lokaci kuma, ana samun karancin ingancin malamai.

“Rashin ingancin koyarwa ya sa dalibai ba za su iya karatu ko yin lissafi ba bayan sun shafe shekaru a makaranta, don magance wannan, dole ne gwamnati ta ba da fifiko ga Ilimi kyauta da yin amfani da fasaha don cike gibin.

Ilimi shi ne ginshikin rage talauci, aikata laifuka, da rashin aikin yi, gina hanyoyin koyar da sana’o’i da kuma samar wa ‘yan Nijeriya makoma nan gaba,” in ji shi.

Wani malami da ke zaune a Abuja, Peter Ojo, ya yi gargadin cewa Nijeriya ba za ta iya kaucewa barazanar da ke kunno kai wacce ‘yan zamani marasa ilimi ke yi ba.

A cewarsa, dangantakar ilimi da ci gaban tattalin arziki ba abu ne da za a iya musantawa ba.

Ya ce, “Ta hanyar ba da fifiko ga ilimi, kasar za ta iya canza matasanta zuwa ga samar da canji mai kyau da ci gaban kasa. Bayan haka, magance duk wata matsala ta zamantakewa ta dogon lokaci dole ne sai an bi ta hanyar ilimi.”

Ya kuma kara bayyana yadda ake fama da karancin kudade a fannin ilimi, inda kashi 7.3 cikin 100 ne kawai na kasafin kudin kasar da aka ware wa ilimi, wanda bai kai kashi 15-20 bisa 100 da hukumar UNESCO ta ba da shawarar ba.

Ya ce rashin kudi a matsayin wani muhimmin al’amari da ke taimaka wa gurbacewar ababen more rayuwa, cunkoson ajujuwa, da rashin isassun kayan koyarwa, rashin wadatar dalibai da malamai da karancin ababen more rayuwa a makarantu duk su ke haifar da wadannan matsaloli.

Sai dai ya amince da ci gaban da wasu jihohin Nijeriya suka samu a baya-bayan nan, kamar su Enugu, Jigawa, Kano, da Kaduna, wadanda suka ware sama da kashi 26 na kasafin kudinsu ga ilimi a shekarar 2025.

A ‘yan kwanakin nan, gwamnatin tarayya da na jihohi da wasu kamfanoni masu zaman kansu na kokarin ganin an shawo kan matsalar yaran da ba sa zuwa makaranta a Nijeriya. A kwanakin baya, babbar sakatariyar hukumar kula da ilimin bai daya ta kasa (UBEC), Aisha Garba, ta ce hukumar za ta fadada rajista da shigar da su cikin tsarin ilimin boko domin rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a kasar nan, musamman a yankunan karkara.

Ta kuma bayyana cewa galibin yaran da ba sa zuwa makaranta suna zaune ne a yankunan karkara kuma aksarinsu ‘ya’yan talakawa ne, inda rashin daidaiton tattalin arziki ke haifar da fatara a gidaje da dama.

Ta kuma jaddada bukatar kara bayar da shawarwari don magance muhimman kalubalen ilimi a Nijeriya.

Har ila yau, gwamnatin tarayya ta kaddamar da wani sabon shiri mai suna ‘Lumina Programme’, na magance yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a Nijeriya.

Karamar ministar ilimi, Farfesa Suwaiba Ahmad Ahmad, ta bayyana cewa shirin zai samar da ilmin karance-karance da kuma ilmin lissafi, musamman ga yara mata a cikin al’ummomin da ke da wuyar isar da sako.

A Kaduna, gwamnatin jihar ta ce za ta horas da mambobin kwamitin kula da makarantu (SBMC) 8,700 domin inganta ilimi a matakin farko a jihar.

Mukaddashin shugaban hukumar kula da ilimin bai daya ta Jihar Kaduna (KADSUBEB) Mubarak Muhammad ne ya bayyana hakan a Kaduna kwanan nan.

Har ila yau, wata kungiya mai zaman kanta (NGO) mai suna IA-Foundation, ta tara Naira miliyan 30 a taron agajin da ta gudanar kwanan nan a birnin Landan domin tallafa wa ilimin yaran da ba sa zuwa makaranta a Nijeriya.

Shugabar kungiyar ta IA-Foundation, Misis Ibironke Adeagbo, ta ce za a tura asusun ne domin taimakawa muhimman ayyukan kungiyar kai tsaye.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Tsaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mayar Da Hankali A Aikin Farfado Da Kwararrun Asibitocin Gwamnatin Tarayyya

Next Post

Ramuwar Gayya: Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Yawa A Borno

Related

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

10 hours ago
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin
Manyan Labarai

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

12 hours ago
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba
Da ɗumi-ɗuminsa

Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

16 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas
Manyan Labarai

‘Yan Kasuwa Na Neman Diyya Bayan Rushe Kasuwar Alaba Rago A Legas

17 hours ago
Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya
Rahotonni

Ranar Hausa: Yadda Hausawa Ke Tunƙaho Da Harshensu A Faɗin Duniya

22 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

1 day ago
Next Post
Ramuwar Gayya: Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Yawa A Borno

Ramuwar Gayya: Sojoji Sun Kashe 'Yan Ta'adda Da Yawa A Borno

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hukumar NRC Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jiragen Kasa Na Abuja zuwa Kaduna

August 26, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

August 26, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

August 26, 2025
Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

August 26, 2025
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.