• English
  • Business News
Saturday, July 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da gwamnatin Amurka mai ci ke kara tsaurara matakan shiga kasar ga baki daga ketare a matakai daban daban, masharhanta na ta bayyana baiken wadannan matakai, wadanda ko shakka babu ba za su haifarwa Amurkan, da ma sauran sassan kasa da kasa ‘da mai ido ba.

A baya bayan nan, mun ga yadda gwamnatin Amurkan ta sanar da cewa baki masu shiga kasar sai sun yi wata rajista ta daban, baya ga biza da suke dauke da ita. Kazalika, tun daga 8 ga watan Yunin nan ta haramtawa al’ummun kasashen Afghanistan, da Myanmar, da Chadi, da Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo, da Equatorial Guinea, da Eritrea, da Haiti, da Iran, da Libya, da Somalia, da Sudan da Yemen damar shiga kasar bisa “wai” dalilai na tsaron kasa.

  • Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi
  • Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

Wadannan matakai, kari ne kan yunkurin da gwamnatin Amurkan ta yi na dakile ikon jami’ar Harvard, na baiwa dalibai da masu zuwa ayyukan bincike damar shiga jamiar. Inda har aka jiyo wasu rahotanni na cewa ma’aikatar tsaron kasar na nazari kan bizar daukacin ’yan kasashen waje wadanda ke da alaka da jami’ar ba wai dalibai kadai ba.

Kafin hakan, gwamnatin Amurka ta ayyana manufar soke damar jami’ar Harvard din ta daukar dalibai daga ketare, da rage kudaden da gwamnatin kasar ke samarwa jami’ar, matakin da wata kotun kasar ta bayyana da haramtacce. Wadannan matakai dukkaninsu na nuni ga yadda gwamnatin Amurka mai ci ke kokarin siyasantar da harkar ilimi, da halastattun hakkokin matafiya na kasa da kasa bisa fakewa da batun tsaron kasa, duk kuwa da cewa ba wasu shaidu na hakika dake nuna wajibcin daukar wadannan matakai.

Alal hakika, bai kamata musayar ilimi, ko hadin gwiwar gudanar da bincike su zama makamin siyasa ba. A hannu guda, tauyewa matafiya damar zirga-zirga tsakanin kasashen duniya ciki har da Amurka, mataki ne na keta hakkokin al’ummun duniya, wanda hakan ke kara fayyace gibin dake akwai, tsakanin kalaman Amurka na fatar baki, da kuma ikirarin da take yawan yi na “wai” tana martaba ’yancin bil adama.

Labarai Masu Nasaba

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Next Post

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Related

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa
Daga Birnin Sin

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

16 hours ago
Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka
Daga Birnin Sin

Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka

17 hours ago
Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Karbi Takardun Nadi Daga Sabbin Jakadun Kasashen Waje

18 hours ago
Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD
Daga Birnin Sin

Wakilin Sin Ya Karyata Amurka Game Da Batun Yankin Xinjiang Na Sin a Taron Kwamitin Sulhun MDD

19 hours ago
Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya
Daga Birnin Sin

Kamfanin Sinotruk Na Kasar Sin Ya Kaddamar Da Sabbin Motocin Dakon Kaya A Kenya

20 hours ago
An Amince Da Biranen Kasar Sin 9 A Matsayin Biranen Dausayi Na Kasa Da Kasa
Daga Birnin Sin

An Amince Da Biranen Kasar Sin 9 A Matsayin Biranen Dausayi Na Kasa Da Kasa

21 hours ago
Next Post
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

LABARAI MASU NASABA

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

Edo Da Taraba : ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 31 Da Aka Yi Garkuwa Da Su Bayan Musayar Wuta

July 26, 2025
WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe

July 26, 2025
Kotu

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

July 26, 2025
Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4

July 26, 2025
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

July 26, 2025
Gwamnatin Kano Ta Gabatar Da Buƙatu 10 A Gaban Kwamitin Gyaran Tsarin Mulkin Nijeriya

Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincikar Kwamishinan Sufuri Kan Karɓar Belin Dilan Ƙwaya A Kano

July 26, 2025
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA

July 26, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

July 26, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

July 26, 2025
Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

July 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.