Akalla mutane goma ne aka tabbatar da mutuwarsu, da suka hada da dalibai da malamai, sakamakon wani mummunan harbe-harbe da aka yi a wata makarantar sakandire a garin Graz na kasar Austriya.
Hukumomin kasar sun ce wanda ake zargi da kai harin, mutum daya ne kuma shi ma ya harbe kansa da kansa.
- Sarki Sanusi II Ya Yi Hawa Duk Da Umarnin ‘Yansanda Na Haramta Hawan Sallah A Kano
- Ƙungiyar G-5 Ta Ceto Nijeriya Daga Faɗa Wa Rikici — Wike
Har yanzu ba a bayyana sunan wanda ake zargin ba, har sai an gudanar da bincike da kuma sanar da danginsa.
Masu bayar da agajin gaggawa sun isa wurin jim kadan bayan karfe 9 na safe, inda hargitsi da firgici ya da baibaye mazauna harabar makarantar.
A cewar ‘yansandan yankin, dan bindigar ya shiga ajin karatun ne dauke da bindiga inda ya bude wuta kan mai uwa da wabi, sannan kuma ya harbe kansa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp