• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasurgumin Dan Bindiga ‘Bello Turji’ Ya Rungumi Zaman Lafiya, Ya Koma Yakar ‘Yan Bindiga – Gwamnati

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Kasurgumin Dan Bindiga ‘Bello Turji’ Ya Rungumi Zaman Lafiya, Ya Koma Yakar ‘Yan Bindiga – Gwamnati
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara, Sanata Hassan Nasiha, ya bayyana cewar gawurtaccen dan bindiga Bello Turji da ya shahara wajen sace mutane, ya saduda ya rungumi zaman lafiya kana ya daina kai hare-hare kan jama’a a kananan hukumomin Birnin Magaji, Shinkafi da Zurmi.

Hassan, ya bayyana hakan ne a wajen wani taro kan tsaro a Gusau babban birnin jihar, wanda kungiyar daliban Jami’ar Madina suka shirya, inda ya ce, shi Bello Turji a bisa radin kansa da kashin kansa ya amince wajen kawo zaman lafiya a kananan hukumomin uku, inda suka kasance wuraren boyar masu garkuwa da mutane da ke kai hare-hare ga jama’a a Jihar Zamfara da shiyyar Arewa Maso Yamma.

  • Sojoji Sun Dakile Yunkurin Kafa Sansanin ‘Yan Bindiga A Jihar Neja
  • El-Rufa’i Ne Silar Matsalar Tsaro A Kaduna – Shehu Sani

A cewar mataimakin gwamnan, Sanata Nasiha, sama da makonni biyar da suka wuce ba a samu fada tsakanin Fulani da Hausawa a kananan hukumomin Birnin Magaji, Shinkafi da Zurmi ba sakamakon rungumar sulhun da ya kawo zaman lafiya tsakanin bangarorin biyu.

Ya bayyana cewar Bello Turji yanzu haka da kansa yake yakar sauran ‘yan bindigar da suka ki rungumar zaman lafiya domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.

A cewarsa, gwamnan Jihar Bello Muhammad, ya kafa kwamiti wanda kuma shi da kansa ke jagoranta sun zauna da ‘yan bindiga da mutane tara a gundumar Magami da Masarautar Dansadau ta Gusau da karamar hukumar Maru, inda suka tattauna kan zaman lafiya tare da nemansu da su daina kai hare-hare ga jama’a.

Labarai Masu Nasaba

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

A cewar Nasiha, gwamna Bello Mohammed, ya umarci cewa dukkanin wuraren kiwo, labi da mashayar dabbobi da wasu kadarorin da aka kwace sakamakon rikici tsakaninsu da Hausawa da a gaggauta maida musu domin farfado da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.

Hassan Nasiha, ya kara da cewa Fulanin suna son gwamnati ta samar musu da taki, a kuma saki Fulanin da suke tsare a gidajen yarin jihar kana a gina wa ‘ya’yansu makarantu.

A cewarsa, samar musu da wadannan bukatun zai taimaka wajen rage musu sha’awar shiga harkokin garkuwa da mutane sakamakon karancin ilimi da ke jefa su cikin wannan abun.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Bello TurjiGarkuwa Da MutaneGusauGwamna Bello Mohammad MatawalleKasurgumin Dan BindigaSanata NasihaSulhuTsafeZaman LafiyaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shin Dalibai Na Da Wakilai A Tattaunawa Tsakanin ASUU Da Gwamnati Kan Yajin Aikin ASUU Kuwa?

Next Post

Korafin Dogara Kan Yunkurin Kasheshi: Muna Kan Bincike Ne Har Yanzu, Amma Mun Kama Mutum Biyu – Kwamishinan ‘Yansanda

Related

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

35 minutes ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

2 hours ago
Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu
Manyan Labarai

Rasuwar Ɗantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya –  Shugaban ƘasaTinubu

4 hours ago
Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe
Manyan Labarai

Bam Ya Kashe Mutane 4, Ya Jikkata 21 A Yobe

5 hours ago
Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa
Manyan Labarai

Hanyar Da Matasa Za Su Bi Don Ceto Demokuradiyyar Nijeriya Daga Rugujewa

6 hours ago
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

11 hours ago
Next Post
Korafin Dogara Kan Yunkurin Kasheshi:  Muna Kan Bincike Ne Har Yanzu, Amma Mun Kama Mutum Biyu – Kwamishinan ‘Yansanda

Korafin Dogara Kan Yunkurin Kasheshi: Muna Kan Bincike Ne Har Yanzu, Amma Mun Kama Mutum Biyu - Kwamishinan 'Yansanda

LABARAI MASU NASABA

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

Sin Ta Samu Nasarorin A Zo A Gani Wajen Yaki Da Miyagun Kwayoyi

June 28, 2025
Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

Kula Da  Kanki Bayan Haihuwa Abu Ne Muhimmi 4

June 28, 2025
Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

Mata Ku Kula Da Masu Tallan Maganin Hana Kishiya

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.