• Leadership Hausa
Monday, February 6, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Manyan Labarai

Kasurgumin Dan Bindiga ‘Bello Turji’ Ya Rungumi Zaman Lafiya, Ya Koma Yakar ‘Yan Bindiga – Gwamnati

by Khalid Idris Doya
6 months ago
in Manyan Labarai
0
Kasurgumin Dan Bindiga ‘Bello Turji’ Ya Rungumi Zaman Lafiya, Ya Koma Yakar ‘Yan Bindiga – Gwamnati

Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara, Sanata Hassan Nasiha, ya bayyana cewar gawurtaccen dan bindiga Bello Turji da ya shahara wajen sace mutane, ya saduda ya rungumi zaman lafiya kana ya daina kai hare-hare kan jama’a a kananan hukumomin Birnin Magaji, Shinkafi da Zurmi.

Hassan, ya bayyana hakan ne a wajen wani taro kan tsaro a Gusau babban birnin jihar, wanda kungiyar daliban Jami’ar Madina suka shirya, inda ya ce, shi Bello Turji a bisa radin kansa da kashin kansa ya amince wajen kawo zaman lafiya a kananan hukumomin uku, inda suka kasance wuraren boyar masu garkuwa da mutane da ke kai hare-hare ga jama’a a Jihar Zamfara da shiyyar Arewa Maso Yamma.

  • Sojoji Sun Dakile Yunkurin Kafa Sansanin ‘Yan Bindiga A Jihar Neja
  • El-Rufa’i Ne Silar Matsalar Tsaro A Kaduna – Shehu Sani

A cewar mataimakin gwamnan, Sanata Nasiha, sama da makonni biyar da suka wuce ba a samu fada tsakanin Fulani da Hausawa a kananan hukumomin Birnin Magaji, Shinkafi da Zurmi ba sakamakon rungumar sulhun da ya kawo zaman lafiya tsakanin bangarorin biyu.

Ya bayyana cewar Bello Turji yanzu haka da kansa yake yakar sauran ‘yan bindigar da suka ki rungumar zaman lafiya domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.

A cewarsa, gwamnan Jihar Bello Muhammad, ya kafa kwamiti wanda kuma shi da kansa ke jagoranta sun zauna da ‘yan bindiga da mutane tara a gundumar Magami da Masarautar Dansadau ta Gusau da karamar hukumar Maru, inda suka tattauna kan zaman lafiya tare da nemansu da su daina kai hare-hare ga jama’a.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kama Wani Da Kokon Kan Mutum A Neja

‘Yan Bindiga Sun Kashe Alkali A Kotu A Jihar Imo

A cewar Nasiha, gwamna Bello Mohammed, ya umarci cewa dukkanin wuraren kiwo, labi da mashayar dabbobi da wasu kadarorin da aka kwace sakamakon rikici tsakaninsu da Hausawa da a gaggauta maida musu domin farfado da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.

Hassan Nasiha, ya kara da cewa Fulanin suna son gwamnati ta samar musu da taki, a kuma saki Fulanin da suke tsare a gidajen yarin jihar kana a gina wa ‘ya’yansu makarantu.

A cewarsa, samar musu da wadannan bukatun zai taimaka wajen rage musu sha’awar shiga harkokin garkuwa da mutane sakamakon karancin ilimi da ke jefa su cikin wannan abun.

Tags: Bello TurjiGarkuwa Da MutaneGusauGwamna Bello Mohammad MatawalleKasurgumin Dan BindigaSanata NasihaSulhuTsafeZaman LafiyaZamfara
Previous Post

Shin Dalibai Na Da Wakilai A Tattaunawa Tsakanin ASUU Da Gwamnati Kan Yajin Aikin ASUU Kuwa?

Next Post

Korafin Dogara Kan Yunkurin Kasheshi: Muna Kan Bincike Ne Har Yanzu, Amma Mun Kama Mutum Biyu – Kwamishinan ‘Yansanda

Related

‘Yansanda Sun Kama Wani Da Kokon Kan Mutum A Neja
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Wani Da Kokon Kan Mutum A Neja

1 day ago
‘Yan Bindiga Sun Kashe Alkali A Kotu A Jihar Imo
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Alkali A Kotu A Jihar Imo

1 day ago
Ba Za A Kara Tsawaita Wa’adin Daina Karbar Tsofaffin Takardun Kudi Ba —Emefiele
Manyan Labarai

Ba Za A Kara Tsawaita Wa’adin Daina Karbar Tsofaffin Takardun Kudi Ba —Emefiele

1 day ago
Akwai  Wasu Kusoshi A Fadar Shugaban Kasa Da Ke Goyon Bayan Atiku – Wike
Manyan Labarai

Akwai  Wasu Kusoshi A Fadar Shugaban Kasa Da Ke Goyon Bayan Atiku – Wike

2 days ago
Canjin Kudi: Ina Sane Da Wahalar Da Mutane Ke Sha, Komai Zai Daidaita – Buhari
Manyan Labarai

Canjin Kudi: Ina Sane Da Wahalar Da Mutane Ke Sha, Komai Zai Daidaita – Buhari

2 days ago
Gwamnonin APC Sun Gana Da Buhari Kan Bukatar Cire Wa’adin Karbar Tsofaffin Kudi
Manyan Labarai

Gwamnonin APC Sun Gana Da Buhari Kan Bukatar Cire Wa’adin Karbar Tsofaffin Kudi

2 days ago
Next Post
Korafin Dogara Kan Yunkurin Kasheshi:  Muna Kan Bincike Ne Har Yanzu, Amma Mun Kama Mutum Biyu – Kwamishinan ‘Yansanda

Korafin Dogara Kan Yunkurin Kasheshi: Muna Kan Bincike Ne Har Yanzu, Amma Mun Kama Mutum Biyu - Kwamishinan 'Yansanda

LABARAI MASU NASABA

Afirka Ba Ta Bukatar Lakca

Afirka Ba Ta Bukatar Lakca

February 5, 2023
Manoman Kwakwa 50 Sun Samu Horo Kan Noman Zamani

Manoman Kwakwa 50 Sun Samu Horo Kan Noman Zamani

February 5, 2023
Sin Na Matukar Adawa Da Matakin Amurka Na Harbo Babban Balan-balan Din Kasar Sin

Sin Na Matukar Adawa Da Matakin Amurka Na Harbo Babban Balan-balan Din Kasar Sin

February 5, 2023
Dalilan Da Ke Hana Kwamfuta Da Wayoyin Hannu Sauri

Dalilan Da Ke Hana Kwamfuta Da Wayoyin Hannu Sauri

February 5, 2023
Ko Mafarkin Samun Gwamna Mace Ta Farko A Nijeriya Zai Zama Gaskiya?

Ko Mafarkin Samun Gwamna Mace Ta Farko A Nijeriya Zai Zama Gaskiya?

February 5, 2023
Shirin Fim Na Tallata Shagalin Murnar Bikin Kunna Fitilu Da CMG Ya Tsara Ya Jawo Hankulan Al’ummar Afirka

Shirin Fim Na Tallata Shagalin Murnar Bikin Kunna Fitilu Da CMG Ya Tsara Ya Jawo Hankulan Al’ummar Afirka

February 5, 2023
An Gudanar Da Jerin Ayyuka Don Murnar Cika Shekara 1 Da Samun Nasarar Gudanar Da Wasannin Olympics Na Lokacin Sanyi Na Beijing

An Gudanar Da Jerin Ayyuka Don Murnar Cika Shekara 1 Da Samun Nasarar Gudanar Da Wasannin Olympics Na Lokacin Sanyi Na Beijing

February 5, 2023
NAHCON Ta Rarraba Kujerun Aikin Hajjin Bana Ga Jihohi 36 Da Abuja

NAHCON Ta Rarraba Kujerun Aikin Hajjin Bana Ga Jihohi 36 Da Abuja

February 5, 2023
Matar Sufeto Ta Gurfanar Da Kurtun Dan Sanda A Kotu Kan Kashe Mijinta

Ya Kashe Makocinsa Don Ya Haske Idon Mahaifiyarsa Da Cocila

February 5, 2023
Gwamnan Jigawa Ya Nada Hameem Nuhu Sanusi Matsayin Sabon Sarkin Dutse

Gwamnan Jigawa Ya Nada Hameem Nuhu Sanusi Matsayin Sabon Sarkin Dutse

February 5, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.