Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya yi kakkausar suka da Allah-wadai da kisan gillar da aka yi wa wani matashi dan shekaru 45, Ahmed Aliyu, wanda aka fi sani da Amadi Kasiran, inda wasu da ake zargin ‘yan daba ne suka kai masa hari tare da kashe shi a unguwar Hammadu Kafi da ke Gombe.
Mummunan lamarin ya faru ne a daren ranar Lahadin da ta gabata, inda aka cakka wa marigayin wuka, kuma daga bisani aka tabbatar da mutuwarsa a asibitin kwararru na Gombe, kamar yadda rahotannin tsaro suka tabbatar.
- Bukatar Kara Yawan Masu Fitowa Kada Kuri’a A Zabuka Nan Gaba
- Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai
Da yake tsokaci kan lamarin, Gwamna Yahaya ya nuna bacin rai da alhininsa, inda ya bayyana kisan a matsayin rashin hankali, kuma abin da sam ba za a lamunta ba.
Ya sha alwashin cewa gwamnatin jihar ba za ta amince da sake dawowar aika-aikar ‘yan kalare da ‘yan daba a Gombe ba, kamar yadda kakakinsa Ismala Uba Misilli ya fitar ta cikin wata sanarwa.
“Wannan mummunan aika-aika ne kai tsaye ga zaman lafiya da tsaron al’ummarmu, a sani, tashin hankali ba shi da gurbi a Jihar Gombe, kuma za mu sanya kafar wando daya da duk wanda aka kama yana tada zaune tsaye,” in ji gwamnan.
Ya umurci jami’an tsaro su gaggauta kai dauki ba tare da bata lokaci ba don tabbatar da an gurfanar da masu laifin a gaban kuliya, yana mai jaddada cewa za a hukunta duk wanda aka samu dauke da muggan makamai ko kuma aka samu yana da hannu wajen aikata laifuka.
“Ga iyalai da ‘yan uwa da masoyan marigayi Ahmed, ina mika sakon ta’aziyyata, da na gwamnati da al’ummar Jihar Gombe, kuma muna jimami tare da ku, ina ba ku tabbacin za a yi adalci.
“Ina kuma kira ga jami’an tsaro su kara kaimi wajen tattara bayanan sirri da kuma sintiri kan tituna, musamman a wuraren da ke fuskantar irin wadannan laifuka. Jama’armu sun cancanci tafiya cikin walwala ba tare da tsoro ko barazana ga rayuka da dukiyoyinsu ba.
“Muna ci gaba da jajircewa wajen kare kowane rai da kuma tabbatar da cewa zaman lafiya da tsaro sun ci gaba da wanzuwa a wannar jiharmu.”
Ya yi kira ga al’umma su tallafa wa jami’an tsaro ta hanyar ba su bayanai masu muhimmanci kan lokaci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp