Hukumar kididdiga ta kasar Sin, ta fitar da wasu alkaluma a Litinin din nan, dake shaida gudanar hada-hadar tattalin arzikin kasar bisa daidaito a watan Mayun da ya gabata. Alkaluman da hukumar ta fitar yayin taron manema labarai, sun nuna ci gaban da aka samu a watan na Mayu, duk kuwa da matsin da aka fuskanta.
Hukumar ta ce an samu daidaito a karuwar samar da hajojin masana’atu, da fadadar bukatunsu, da guraben ayyukan yi, kana an samu ci gaba mai inganci dake kara kusantar managarcin ci gaba da kirkire-kirkire.
Kazalila, alkaluman sun shaida yadda sashen masana’antun sarrafa hajoji ke kara bunkasa bisa daidaito, inda sashen sarrafa manyan kayayyakin aiki, da na masana’antun fasahohin zamani ke kara fadada cikin sauri. Bugu da kari, kasar Sin ta samu ci gaba a fannin sana’o’in samar da hidimomi. Inda a watan na Mayu, alkaluman ci gaban sana’o’in samar da hidimomin ya karu da kaso 6.2 bisa dari a mizanin shekara-shekara, wato an samu karin saurin kaso 0.2 bisa dari sama da wanda aka gani a watan Afirilu.
A daya bangaren kuma, yanayin sayayya ya farfado sosai, yayin da aka samu karuwar musayar sabbi da tsofaffin kayayyaki bisa rangwamen da gwamnati ta samar. Kana darajar sayayyar daidaikun kayayyakin bukatun yau da kullum ta kai kudin Sin yuan biliyan 4,132.6, karuwar da ta kai ta kaso 6.4 bida dari a mizanin shekara-shekara. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp