Wasu ‘yan bindiga sun kai hari ƙauyen Tadurga da ke ƙaramar hukumar Zuru a Jihar Kebbi a dare ranar Litinin, inda suka kashe mutane da dama, suka yi garkuwa da wasu, sannan suka sace shanu.
Wani mazaunin ƙauyen, Audu Sule, ya ce ‘yan bindigar sun zo da yawansu, suna harbi ba ƙaƙƙautaws, lamarin da ya tayar da hankalin jama’a.
- Dalilin Da Ya Sa Sin Ta Samu Bunkasar Tattalin Arziki Mai Dorewa Duk Da Kalubalolin Da Ake Fuskanta A Duniya
- Xi Da Shugabannin Kasashe 5 Na Tsakiyar Asiya Sun Halarci Bikin Rattaba Hannu
Haka kuma sun shiga shaguna suka kwashe kaya.
“Sun zo da makamai suna harbi ko’ina, sun shiga shaguna suka kwashe kayayyaki, suka kashe mutane da dama, suka tafi da wasu sannan suka sace shanunmu,” in ji Sule.
Ya ce wannan hari ya firgita mutane sosai, kuma shi ne mafi muni da suka gani tun bayan hawan Gwamna Nasir Idris kan mulki.
Wani mazaunin yankin, Abdullah Zuru, ya ce yankin ya samu zaman lafiya a baya, inda manoma suka koma gonakinsu kafin wannan mummunan hari.
Kakakin rundunar ‘yansandan Jihar Kebbi, Nafiu Abubakar, bai amsa kiran wayar da aka yi masa ba dangane da harin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp