A ƙalla mutane 24 sun mutu a hare-haren da ‘yan bindiga suka kai a ƙananan hukumomin Kankara da Sabuwa na jihar Katsina cikin mako guda. Waɗanda abin ya shafa sun haɗa da manoma 20, mazauna uku, da wani Bijilantin guda.
Majiyoyi sun bayyana cewa maharan sun kai hari a ƙauyuka kamar Yargoje, Kwakware, da Marmara, inda suka kashe mutane, suka sace wasu, tare da sace dabbobin gida. A wani hari a ƙauyen Marmara, ‘yan bindiga sun kashe ɗan Bijilanti (Civilian JTF) kuma sun jikkata wasu Civilian JTF biyu.
- An Kashe Wasu ‘Yan Bindiga 12, An Kwato Makamai A Katsina
- ‘Yan Bindiga Sun Kashe Jami’an Tsaro 4 Da Manoma A Katsina
A ranar 18 ga Yuni, Ƴansandan Katsina sun ce sun ceto mata uku da wata yarinya ‘yar shekara ɗaya a yunƙurin sace su da aka yi a ƙauyen Mazare. Sun kuma jikkata mazauna biyu yayin da suka yi artabu da maharan.
Wani mazaunin Kankara ya danganta ƙaruwar hare-haren da rashin daidaiton yarjejeniyar zaman lafiya a yankin. “Idan aka yi sulhu a wasu wuraren kuma a wasu ba’a yi ba, ‘yan bindiga za su ci gaba da kai hare-hare,” in ji majiyyar.
Hukumar ‘yansandan ta tabbatar da cewa waɗanda aka ceto ba su ji rauni ba, yayin da waɗanda aka jikkata ke ci gaba da samun kulawa a asibiti. Jihar Katsina ta kasance ɗaya daga cikin jihohin da ke fuskantar hare-haren ‘yan bindiga akai-akai.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp