• English
  • Business News
Tuesday, June 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump

by Sadiq
15 hours ago
in Kasashen Ketare, Manyan Labarai
0
Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce Iran da Isra’ila sun amince su dakatar da yaƙi a tsakaninsu.

Ya sanar da haka ne a shafinsa na sada zumunta, inda ya ce Iran ce za ta fara dakatar da kai hare-hare, daga bisani kuma Isra’ila za ta bi sahu.

  • Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi
  • Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Ayyukan Kiwon Lafiya Kyauta Ga Yara A Botswana

A halin yanzu dai Isra’ila tana ci gaba da kai hari kan Iran, kamar yadda ministan tsaronta ya faɗa, yayin da Iran ta gargaɗi mutanen garin Ramat Gan kusa da Tel Aviv da su bar wajen saboda yiwuwar kai hari.

Trump ya ce tsagaita wutar za ta fara aiki cikin awa shida, kuma daga nan zuwa awa 24 yaƙin zai ƙare gaba ɗaya.

Shin sun tsagaita da gaske?

Labarai Masu Nasaba

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

Sai dai babu wani tabbaci daga gwamnatin Iran ko Isra’ila kan cewa sun yarda su dakatar da yaƙin.

Trump ya kira rikicin da ake ciki da suna “yaƙin kwana 12,” yana mai cewa wannan rikici da za a iya yin shekaru ana fafatawa da shi bai bazu ba, kuma ba zai bazu ba.

Mene ne ke faruwa yanzu?

Bayan da Trump ya sanar da cewa an tsagaita wuta, Isra’ila ta ce an kashe mutane uku sakamakon hare-haren da Iran ta kai.

Amma ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi, ya ce babu wata yarjejeniya ta tsagaita wuta.

Sai dai ya ce Iran za ta daina kai hari idan Isra’ila ma ta dakatar da nata.

Rikicin ya tsananta ne bayan Iran ta kai hari sansanin sojin Amurka da ke Qatar, wanda ya sa Trump ya nemi a dakatar da faɗan.

Me Iran da Isra’ila suka ce?

Gidan talabijin na Iran (IRINN) ya ce an tsagaita wuta ne bayan da Iran ta samu nasara a harin da ta kai.

Sun ce Trump ne ya roƙi a daina faɗam.

Ministan harkokin wajen Iran ya ce Iran ta daina kai hari tun ƙarfe 4 na dare, idan har Isra’ila za ta daina nata.

Har yanzu Isra’ila ba ta fitar da wata sanarwa ba kan tsagaita wutar, sai dai bayan sanarwar Trump, Isra’ila ta sake kai hari Iran.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: IranIsra'ilaTrumpyaƙi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi

Next Post

Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Mako 3

Related

Sabbin Ministoci
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

5 hours ago
Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC
Manyan Labarai

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

8 hours ago
An Cafke Mutum 22 Kan Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato – Uba Sani
Manyan Labarai

An Cafke Mutum 22 Kan Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato – Uba Sani

13 hours ago
Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Mako 3
Manyan Labarai

Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Mako 3

15 hours ago
Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi

23 hours ago
Karin Kudin Mai: Hakika An Ci Amanarmu, In Ji ‘Yan Kwadago
Manyan Labarai

NNPC Ya Ƙara Kuɗin Fetur, Duba Sabon Farashin

1 day ago
Next Post
Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Mako 3

Sojoji Sun Hallaka 'Yan Ta'adda 600 Cikin Mako 3

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

June 24, 2025
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

June 24, 2025
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

June 24, 2025
Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

June 24, 2025
Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

June 24, 2025
Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

June 24, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

June 24, 2025
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

June 24, 2025
Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

June 24, 2025
Sabuwar Shugabar Kwamitin Wasannin Olympics Na Duniya Na Fatan Sake Ziyartar Kasar Sin

Sabuwar Shugabar Kwamitin Wasannin Olympics Na Duniya Na Fatan Sake Ziyartar Kasar Sin

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.