Ƙungiyoyin ƙwallon ƙafa na Manchester United da Everton sun nuna sha’awarsu na ɗaukar ɗan wasan Nijeriya Wilfred Ndidi, wanda ke buga wasa a Leicester City.
Ndidi yana son barin Leicester City tun da ƙungiyar ta sauka daga gasar Firimiyar Ingila zuwa Championship a bara.
- KAROTA Ta Kama Matasa 5 Kan Ɗaukar Bidiyo A Kan Hanya A Kano
- Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?
Duk da haka, ya sake sabunta kwantiragin shekaru uku da Leicester a baya.
Duk wata ƙungiya da ke son ɗaukar Ndidi daga Leicester dole ne ta biya fam miliyan tara, kamar yadda yarjejeniyarsa ta nuna.
A bara, Everton ta so sayen Ndidi, amma bai yarda ba.
Yanzu sun sake nuna sha’awarsu, suna fatan ɗaukar ɗan wasan mai shekaru 28.
Manchester United ma ta nuna sha’awar ɗaukar Ndidi idan har ta sayar da Casemiro, wanda ake raɗe-raɗin zai koma Saudiyya.
A watan Janairu, Monaco da ke gasar Ligue 1 ta yi ƙoƙarin ɗaukar Ndidi, amma Leicester ta ƙi amincewa.
Hakazalika, akwai ƙungiyoyi daga Saudiyya da ke son ɗaukarsa kuma suna shirin ba shi albashi mai tsoka, amma Ndidi yafi son ci gaba da buga wasa a Turai.
Ndidi ya koma Leicester City a watan Janairun 2017 daga kulob ɗin Genk na Belgium.
Ya lashe kofin FA Cup da Leicester a 2020, kuma ya zura ƙwallaye 11 a cikin wasanni 252 da ya buga wa ƙungiyar cikin shekaru takwas.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp