Gwamnatin tarayya ta sanar da cewa, Nijeriya ta kai wani mataki a duniya a bangaren samar da wadatacciyar Madarar Shanu.
Burin kasar a yanzu shi ne, samar da Madara ta kimanin dala biliyan 1.5, wacce kuma za a rika fitar da ita zuwa kasashen ketare a duk shekara tare da kuma da samar da wadda ake bukata a cikin kasar, wadda yawanta ya kai kimanin tan 1.5, (Lita biliyan 1.5) a duk shekara.
- Har Yanzu Da Akwai Jihohin Da Malaman Makaranta Ke Karbar Albashin Naira 18,000
- Abba Ya Dace Ya Zama Gwamnan Kano Na Har Abada Ba Shekaru 8 Kaɗai Ba – Arch Ali Hassan
A halin yanzu, kasar na samar da akalla tan 700,000 na madara a duk shekara, idan aka kwatanta da tan miliyan 1.6 da ake amfani da ita, inda a duk shekara ake kashe sama da dala biliyan 1.5 wajen shigo da madarar; wanda hakan ya kai saura kashi 60 cikin 100.
Ministan Ma’aikatar Bunkasa Kiwon Dabbobi, Alhaji Idi Mukhtar Maiha, a jawabinsa ranar bikin madarar Shanu ta duniya da aka gudanar a kwanakin baya a Abuja ya bayyana cewa, akwai bukatar a cike gibin da ake da shi na samar da madarar nan da shekaru biyar masu zuwa.
“Nijeriya ba wai kawai ta na da burin kamo duniya wajen samar da madarar ba ne, amma tana da burin kasancewa kan gaba wajen samar da madarar,“ in ji Mukhtar.
“Abin da muke son cimma shi ne, a duk shekara mu tabbatar da ganin mun rubanya yawan madarar da ake samarwa kasar a kasar daga tan miliyan 700,000 zuwa tan miliyan 1.4 daga nan zuwa shekara biyar masu zuwa”, a cewar Ministan.
“A Nijeriya akwai sama da Shanu miliyan 20.9, Tumaki sama da miliyan 60, Awakai sama da miliyan 1.4”, in ji shi.
Kazalika, Minstan ya kara da cewa; burin shi ne ganin an kara bunkasa tattalin arzikin kasar tare da kuma kara samar da ayyukan yi ga ‘yan kasar.
“Ina son fayyace cewa, ba wai batu ne kawai na yawan Shanun da ake da su a kasar nan ba, batu ne na jama’a da samar da ayyukan yi, habaka kasuwanci da kuma kara daga kimar tattalin arzikin kasar da kuma samar da madarar da za ta gina jikin yara kanana”, a cewar tasa.
Ministan ya ci gaba da cewa, wannan batu ne na matasan kasar da suke da burin fara yin sana’ar sarrafa madarar Yagot.
Ya kara da cewa, tuni gwamnatin tarayya cikin watanni biyu da suka gabata ta hanyar yin amfani da cibiyar gudanar da bincike ta kiwon dabbobi da ke garin Zariya a Jihar Kaduna, ta fara yin rijistar wasu nau’ika takwas na ciyawar da ake ciyar da dabbobi, wanda wannan aiki shi ne karo na farko a cikin shekaru 48 da suka wuce a fadin kasar nan.
Ministan ya bukaci daukacin matasan kasar nan, da su yi amfani da fasahar da suke da ita da kuma samar da dabaru, musamman domin kara ciyar da fannin na samar da madarar Shanun a wannan kasa.
“Muna da bukatar samar da wata kafar sadarwa da za ta rika sada masu sarrafa madara a kasar, musamman domin kara samar musu da kasuwa da kuma masu bayar da daukin kudade a fannin na samar da madara,” a cewar Ministan.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp