ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tetfund Ta Samar Da Naira Biliyan 100 Don Inganta Ilimin Likitanci – Masari

by Rabi'u Ali Indabawa
10 months ago
Masari

Shugaban Asusun Tallafa Wa Manyan Makarantu (TETFund), Rt. Hon. Aminu Bello Masari, ya ce hukumar gudanarwar hukumar ta amince da fitar da sama da Naira biliyan 100 ga manyan makarantun kasar nan domin bunkasa kokarinsu na horar da dalibai kan ilimin likitanci.

Aminu Bello Masari ya bayyana haka a wata tattaunawa da manema labarai a Katsina.

  • Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare
  • Salon Zamanantarwa Na Sin Kyakkyawan Misali Ne Ga Kasashen Afirka

A cewarsa, an dauki matakin ne saboda muradin shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu na ganin an magance karancin ma’aikata a fannin kiwon lafiya da kuma hana wasu guduwa zuwa wasu kasashe.

ADVERTISEMENT

“Shugaban kasa ya damu musamman da yanayin da kuma yadda lamarin ke shafar tsarin kiwon lafiyar Nijeriya, yana so ya kafa matakan da za su ba da damar farfado da tsarin kiwon lafiya ta hanyar tsare-tsare irin wannan shiga tsakani na TETFUnd.

“Mun zabo manyan makarantu guda uku a kowace shiyyar siyasar kasar nan, inda kowace cibiya ta karbi Naira biliyan 4 don gudanar da ayyuka da fadada ilimi musamman don kara karfin daukar dalibai da horar da dalibai a fannin ilimin likitanci.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

“Manufar ita ce a ninka adadin likitoci, ma’aikatan jinya, masu hada magunguna, kwararrun dakunan gwaje-gwaje da sauran kwararru a fannin kiwon lafiya. Wannan ko shakka babu zai kara habaka harkokin kiwon lafiya a kasar,” in ji shi.

Tsohon gwamnan Jihar Katsinan ya bayyana cewa, a bana, TETFund ta samu tallafinta mafi girma na Naira Tiriliyan 1.6, wanda ya haura daga kaso 3 na harajin ilimi da aka dora wa ribar kamfanonin da ke kasuwanci a Nijeriya kamar yadda dokar TETFund ta tanada.

Masari ya bayyana cewa, daga cikin Naira Tiriliyan 1.65, an fitar da Naira biliyan 225 zuwa asusun bayar da lamuni na ilimi na Nijeriya (NELFUND), domin shirin rancen daliban gwamnatin tarayya.

Masari
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    ‘Ƴan Bindiga Sun Hana Manoman Sakkwato Zuwa Gonakinsu, Sun Ƙaƙaba Sabbin Haraji
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Matsalar Tsaro:Kashi 60 Na Masana’antu A Arewa Maso Gabas Sun Durƙushe

MASU ALAKA

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina
Labarai

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

June 20, 2026
Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
Labarai

Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

June 20, 2026
Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina
Labarai

Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

June 20, 2026
Next Post
Firaministan Sin Ya Bukaci A Zage Damtse Wajen Bude Sabon Babin Gina Wayewar Kai Ta Fuskar Kare Muhallin Halittu A Sabon Zamani

Firaministan Sin Ya Bukaci A Zage Damtse Wajen Bude Sabon Babin Gina Wayewar Kai Ta Fuskar Kare Muhallin Halittu A Sabon Zamani

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

Sojoji Sun Yi Wa Ƴan Bindiga Mummunar Barna A Katsina

June 20, 2026
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

June 20, 2026
Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya

June 20, 2026
Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu

June 20, 2026
Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

Hijira 1448:Za A Samu Yalwar Tattalin Arziƙi A Nijeriya —Sheikh Muhajjadina

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya

Turkiyya Ta Zama Ƙasa Ta Biyu Da Ta Fice Daga Gasar Kofin Duniya

June 20, 2026
2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa

June 20, 2026
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

NPA Ta Samar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Da Za Su Ƙarfafa Kasuwanci Da Ƙasashen Duniya – Dantsoho

June 20, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.