• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

by Sulaiman
11 hours ago
in Labarai
0
Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya bayyana cewa Shirin Sabunta Fata na Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu yana samar da damarmaki na cigaban ƙasa a fannoni daban-daban na tattalin arzikin Nijeriya.

 

Ministan ya bayyana haka ne a ranar Alhamis a Minna, Jihar Neja, yayin taron Kwamishinonin Yaɗa Labarai daga jihohin da jam’iyyar APC take mulki, wanda Ƙungiyar Gwamnonin APC ta shirya don ƙarfafa dabarun sadarwa da haɗin gwiwa tsakanin matakai daban-daban na gwamnati.

  • Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Kai Matakin Kwata Fainal Bayan Doke Botswana
  • Sauye-sauyen Tinubu Suna Taimaka Wa Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya — Minista

Ya ce: “Shirin Sabunta Fata ya wuce sauye-sauyen tattalin arzikin ƙasa gaba ɗaya. Magana ce ta samar da damarmakin cigaban ƙasa a fannoni daban-daban – ga mutum ɗaya, ga iyalai, da kuma ga al’umma gaba ɗaya.”

 

Labarai Masu Nasaba

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

Ya bayyana cewa gwamnatin Tinubu tana aiwatar da shirye-shirye masu ɗaukar hankali ta hanyar manyan ayyukan gine-gine, shirye-shiryen tallafa wa matasa, da kuma sauye-sauye a fannonin noma, makamashi, ilimi da ƙere-ƙere.

 

Ministan ya bayyana cire tallafin fetur a matsayin ɗaya daga cikin manyan matakan da gwamnatin ta ɗauka domin farfaɗo da tattalin arziki.

 

Ya ce: “Ɗaya daga cikin manya kuma mafi tasiri daga cikin matakan da wannan gwamnati ta ɗauka shi ne cire tallafin fetur, wanda ko da yake ya kasance mai raɗaɗi, amma sauyi ne da ya zama dole. Bayan ceton tattalin arzikin ƙasa daga rugujewa, wannan mataki ya hana ɓarna da asarar kuɗi sosai a tattalin arzikin mu.”

 

A cewar sa, kuɗaɗen da aka ceto daga cire tallafin ana amfani da su ne wajen manyan ayyukan raya ƙasa irin su hanyar Legas zuwa Kalaba, hanyar Sakkwato zuwa Badagiri, shimfiɗa layin dogo na Kaduna zuwa Kano, da sake gina hanyar mota ta Abuja zuwa Kaduna da Kano.

 

Ya ƙara da cewa akwai cigaba da aka samu wajen saka hannun jari a fannin ayyukan jin daɗi a faɗin ƙasar nan, tare da ƙaruwa a cikin kuɗaɗen da ake tura wa jihohi a kowane wata, wanda ke ba su damar aiwatar da ayyuka masu tasiri a matakin jiha da ƙananan hukumomi.

 

Dangane da shirye-shiryen tallafa wa jama’a, Idris ya bayyana cewa sama da ƙananan harkokin kasuwanci 900,000 sun riga sun amfana daga Shirin Tallafi da Lamunin Shugaban Ƙasa, yayin da sama da ɗalibai 350,000 suke amfana da lamunin karatu domin tabbatar da cewa babu matashin da zai kasa karatu sakamakon rashin kuɗi.

 

Ya bayyana cewa gwamnati ta ware kimanin naira biliyan 70 don lamunin karatu, wanda sama da matasa 600,000 suke neman amfana da shirin.

 

Ministan ya kuma bayyana ƙirƙirar Hukummomin Cigaban Yankuna a faɗin ƙasar nan da cewa wani mataki ne da Shugaban Ƙasa Tinubu ya ɗauka domin tabbatar da cigaba bisa yanayin kowane yanki daga cikin yankunan siyasa shida na ƙasar nan.

 

Ya ce aikin bututun gas ɗin Ajakuta zuwa Kaduna da Kano (AKK) yana tafiya yadda ya kamata, kuma zai bai wa masana’antu da ke kan wannan hanya wutar lantarki domin farfaɗo da masana’antu.

 

Ya ce: “Da zarar an kammala aikin, zai kawo wutar lantarki daga Ajakuta zuwa Kaduna da Kano. Wannan yana nufin cewa dukkan masana’antun da ke kan wannan layi za a farfaɗo da su.”

 

Idris ya bayyana gwamnatin Tinubu a matsayin gwamnati mai ɗaukar rayuwar matasa da muhimmanci, inda ya ambaci shigar matasa da dama cikin Majalisar Zartarwa ta Tarayya a matsayin ministoci da kuma wasu muƙamai a hukumomin gwamnati.

 

Ya ƙara da cewa gwamnatin tana kashe naira biliyan 75 ta hanyar Bankin Masana’antu (BOI) domin tallafa wa ƙanana da matsakaitan masana’antu a fannoni daban-daban da nufin samar da ayyukan yi da kuma ƙarfafa matasa.

 

Ya ce: “Waɗannan ba wai wasu alƙaluma ne kawai marasa ma’ana ko maganganu na manufofi ba. Waɗannan damarmaki ne—damarmaki na zahiri, waɗanda za a iya auna su, ga kowane ɗan Nijeriya.”

 

Idris ya yi kira ga Kwamishinonin Yaɗa Labarai na jihohi da su ɗauki nauyin isar da saƙon da ya shafi manufofin gwamnati ga jama’a da kuma fahimtar yadda za su amfana da su.

 

Ya ce: “Saboda haka, nauyin mu ne a matsayin masu kula da yaɗa labarai, mu tabbatar da cewa ‘yan ƙasa a faɗin jihohin tarayya ba kawai sun san da waɗannan sauye-sauye da shirye-shirye ba ne, amma su ma fahimci yadda za su iya samun dama su amfana da su.”

 

Ya shawarci kwamishinonin da su koma jihohin su da sabon ƙwazo, su yi amfani da Hukumar Wayar da Kai ta Ƙasa (NOA) da kuma haɗin gwiwa da masu ruwa da tsaki na cikin gida domin fassara shirye-shiryen Gwamnatin Tarayya zuwa ayyuka masu amfani a matakin ƙasa.

 

Taron, wanda Gwamnatin Jihar Neja ta karɓi baƙuncin sa, ya haɗa kwamishinonin yaɗa labarai daga jihohin APC domin ƙarfafa dabarun sadarwa da kuma inganta haɗin gwiwa wajen aiwatar da Shirin Sabunta Fata a matakin jihohi da ƙananan hukumomi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

Next Post

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

Related

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
Ra'ayi Riga

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

14 minutes ago
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a
Rahotonni

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

59 minutes ago
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa
Labarai

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

3 hours ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

4 hours ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Labarai

Amurka Ta Rage Wa’adin Bizar ‘Yan Nijeriya Zuwa Wata Uku

5 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

6 hours ago
Next Post
NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

LABARAI MASU NASABA

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

July 11, 2025
FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

July 11, 2025
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

July 11, 2025
Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (2)

Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (2)

July 11, 2025
An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama

An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama

July 11, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Amurka Ta Rage Wa’adin Bizar ‘Yan Nijeriya Zuwa Wata Uku

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.