• English
  • Business News
Thursday, July 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

EU, Turkiyya Da Sauran Ƙasashe Sun Yi Ta’aziyyar Rasuwar Buhari

by Sadiq
19 hours ago
in Manyan Labarai
0
Kasa Da Wata Biyu Ya Bar Mulki, Shin Ko Buhari Ya Cika Wa ‘Yan Nijeriya Alkawarin Da Ya Yi Mu Su?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ƙungiyoyi da ƙasashen duniya sun yi jimami da ta’aziyyar rasuwar tsohon Shugaban Nijeriya, Muhammadu Buhari, wanda ya rasu a wani asibiti da ke birnin Landan a ranar Lahadi, kuma aka binne shi a ranar Talata a garinsu Daura, Jihar Katsina.

Ofishin Tarayyar Turai (EU) a Nujeriya ya wallafa saƙon ta’aziyyarsa a kafar sada zumunta.

  • Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9
  • Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

EU ta yaba wa Buhari bisa shekara takwas da ya yi yana shugabancin Nijeriya, inda ta ce yana da kishin haɗin gwiwar ƙasa da ƙasa da bin doka a harkokin duniya.

“EU na miƙa ta’aziyyarta ta musamman ga al’ummar Nijeriya bisa rasuwar tsohon Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari. A lokacin mulkinsa, Buhari ya nuna goyon baya ga haɗin gwiwa da kuma tsarin dokokin duniya,” in ji sanarwar.

Haka kuma, ofishin jakadancin Turkiyya a Abuja ya miƙa saƙon ta’aziyyarsa ga Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili

Peter Obi Ya Kai Wa Iyalan Buhari Ziyarar Ta’aziyya

Jakadan Turkiyya a Nijeriya, Mehmet Poroy, ya yi masa addu’a domin samun rahamar Allah.

Tun da farko, Ofishin Jakadancin Amurka a Nijeriya ya fitar da sanarwa a shafinsa X, inda ya miƙa ta’aziyya ga ’yan Nijeriya bisa rasuwar tsohon shugaban.

Sanarwar ta ce rayuwar Buhari cike ta ke da hidima, ladabi da jajircewa wajen gaskiya a shugabanci.

Gwamnatin ƙasar China ma ta miƙa saƙon ta’aziyyarta ta hannun ofishin jakadancinta da ke Abuja a shafin X a ranar Lahadi.

Sun yaba wa Buhari tare da nuna baƙin ciki game da rasuwarsa.

Sanarwar ta ce: “Ofishin jakadancin ƙasar China a Nijeriya na miƙa ta’aziyyarsa ta musamman ga al’ummar Nijeriya bisa rasuwar tsohon Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariEURasuwaTurkiyya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Yi Nasarar Harba Kumbon Dakon Kaya Na Tianzhou-9

Next Post

Yara 2 Sun Kuɓuta Bayan Shafe Shekaru 6 A Hannun Boko Haram A Borno

Related

Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili
Manyan Labarai

Atiku Abubakar Ya Fice Daga PDP, Duba Dalili

10 hours ago
Peter Obi Ya Kai Wa Iyalan Buhari Ziyarar Ta’aziyya
Manyan Labarai

Peter Obi Ya Kai Wa Iyalan Buhari Ziyarar Ta’aziyya

11 hours ago
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi
Manyan Labarai

Omokri Da Sarki Sun Soki Obi Saboda Rashin Halartar Jana’izar Buhari

13 hours ago
Kotu Ta Wanke Fayose Daga Zargin Zambar Naira Biliyan 3.3
Manyan Labarai

Kotu Ta Wanke Fayose Daga Zargin Zambar Naira Biliyan 3.3

15 hours ago
Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura
Manyan Labarai

Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura

1 day ago
Da Ɗumi-Ɗumi: Shettima Ya Isa Katsina Da Gawar Buhari
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-Ɗumi: Shettima Ya Isa Katsina Da Gawar Buhari

1 day ago
Next Post
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Yara 2 Sun Kuɓuta Bayan Shafe Shekaru 6 A Hannun Boko Haram A Borno

LABARAI MASU NASABA

Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kafa Makomar Halittun Duniya Ta Bai Daya

Wakilin Sin Ya Yi Kira Da A Kafa Makomar Halittun Duniya Ta Bai Daya

July 16, 2025
Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

Sojoji Sun Kashe Kwamandan Ƙungiyar Haram/ISWAP Da Wasu 5 A Chadi

July 16, 2025
Zambia Na Maraba Da Tawaga Ta 26 Ta Jami’an Lafiya Ta Sin

Zambia Na Maraba Da Tawaga Ta 26 Ta Jami’an Lafiya Ta Sin

July 16, 2025
Dubun Wasu Mutane 20 Da Ake Zargi Da Safarar Makamai A Kwara Ta Cika

Dubun Wasu Mutane 20 Da Ake Zargi Da Safarar Makamai A Kwara Ta Cika

July 16, 2025
Jarin Kasar Sin Ya Bada Gudunmawa Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Zimbabwe

Jarin Kasar Sin Ya Bada Gudunmawa Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Zimbabwe

July 16, 2025
Kwalejin Digiri Na Biyu Ta ABU Ta Ƙaddamar Da Sabbin Ɗalibai A Zariya

Kwalejin Digiri Na Biyu Ta ABU Ta Ƙaddamar Da Sabbin Ɗalibai A Zariya

July 16, 2025
An Gudanar Da Taron Ministocin Wajen Kasashe Mambobin SCO A Tianjin

An Gudanar Da Taron Ministocin Wajen Kasashe Mambobin SCO A Tianjin

July 16, 2025
PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

PDP Ba Za Ta Damu Da Rashin Atiku Ba – Gwamna Makinde

July 16, 2025
Fasahar Amfani Da ’Yan Sandan Mutum-Mutumi Ta Kasar Sin Na Iya Taimaka Wa Tsaro A Afirka

Fasahar Amfani Da ’Yan Sandan Mutum-Mutumi Ta Kasar Sin Na Iya Taimaka Wa Tsaro A Afirka

July 16, 2025
Farashin Kayayyaki Sun Sauka A Watan Yuni 2025

Farashin Kayayyaki Sun Sauka A Watan Yuni 2025

July 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.