• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Banza Man Kare: Barazana Da Takunkumi Sun Daina Tasiri

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago
in Daga Birnin Sin
0
A Banza Man Kare: Barazana Da Takunkumi Sun Daina Tasiri
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Yanzu shekarar ta 2025 muke ciki, kuma matakin da duniya ke daukawa wajen gudanar da al’amura ya bambanta da shekaru goma da suka gabata. Amma abin takaici shi ne, wasu har yanzu sun nace ma tsoffin dabaru, suna ganin barazanar haraji da takunkumi na iya mamaye duniya, na san kun riga kun san inda na dosa. Shugaban Amurka Donald Trump da aka rantsar a baya-bayan nan ya yi barazanar sanya harajin kashi 100 bisa 100 kan kasashen BRICS idan suka ci gaba da kokarin rage tasirin dala. “A matsayinsu na al’ummar BRICS, za a kakaba musu harajin kashi 100 bisa 100 idan har suna tunanin aiwatar da abin da suke tunani, don haka za su yi watsi da hakan nan take.” Wannan na daga cikin kalamansa a ranar farko da ya hau kan karagar mulki. Muna iya cewa wannan na daya daga cikin sumbatunsa da ya saba yi, saboda sanin kowa ne cewa, ba a kafa BRICS don ta yi jayayya, ko sa-in-sa da kowa ba, sai dai don karfafa hadin gwiwa da samun wadata, kuma gaskiyar magana ita ce, yanzu kasashen duniya sun daina tsoron mamayar kudin wata kasa ko matsin lamba na takunkumi.

Mu dauki Rasha a matayin misali, lokacin da ta fuskanci dimbin takunkumi daga kasashen yamma a 2014 da 2022, da yawa sun yi hasashen durkushewar tattalin arzikinta. Maimakon haka, Rasha ta samar wa kanta mafita ta hanyar tsarin hada-hadar kudi na cikin gida wato SPFS, wanda ba ya bukatar tsarin hada-hadar kudi na yammacin duniya, wannan yunkurin ya yi wa tattalin arzikin Rasha garkuwa tare da aza harsashi na zurfafa dangantakar hada-hadar kudi da kawayenta kamar Turkiya, Kazakhstan, har ma da al’ummomi a Gabas ta Tsakiya, tare da yin watsi da tsarin kasashen Yamma. Hakazalika, Amurka ta hana Turkiya damar amfani da fasaha da wasu kayayyakin aiki na Amurka, kama daga jiragen F-35 zuwa jiragen sama marasa matuka. Sakamakon haka shi ne, a halin yanzu Turkiya na kera wasu daga cikin wadannan kayayyakin aiki da albarkatunta har ma ta fara fitar da kayayyaki zuwa wasu kasashen Gabas ta Tsakiya da Afirka. Haka ma kasashen BRICS su ma sun yi ta sake fasalin ka’idojin cinikayyar duniya. Sun koma ga amfani da nasu kudade wajen gudanar da kasuwanci a tsakaninsu, suna rage dogaro da dalar Amurka. Hakazalika, Brazil da Sin na yin cinikayya da kudaden kasashensu, matakin da Indiya da kawayenta na yankin suke koyi da su. Yanzu dai kan mage ya waye, kuma kasashen duniya sun fahimci cewa hadin gwiwar samun moriyar juna tare da dunkulewar duniya waje guda su ne mafita ga kalubalen da duniya ke fuskanta, kuma wannan shi ne makasudin kafa BRICS. (Mohammed Yahaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Lokaci Ya Yi Da Za A Kawo Karshen Fashewar Tankar Mai A Nijeriya – Shettima

Next Post

Firaministan Sin Ya Tattauna Da Baki Kwararru Dake Kasar

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

15 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

16 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

18 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

21 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

22 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

23 hours ago
Next Post
Firaministan Sin Ya Tattauna Da Baki Kwararru Dake Kasar

Firaministan Sin Ya Tattauna Da Baki Kwararru Dake Kasar

LABARAI MASU NASABA

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.