ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, November 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Daɗe Ana Yi Sai Gaskiya

by CMG Hausa
2 years ago
Gaskiya

Shekarar 2023 ta cika shekaru 20 da kulla dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare tsakanin Sin da ƙungiyar ASEAN wato ƙungiyar ƙasashen kudu maso gabashin Asiya, da kuma cika shekaru 20 da kafuwar baje kolin Sin da ASEAN. Wannan ya ba da muhimmiyar ma’ana ga bikin baje kolin Sin da ASEAN na bana, wanda aka bude a ranar 17 ga watan Satumba a birnin Nanning na jihar Guangxi ta kabilar Zhuang mai cin gashin kanta ta kudancin ƙasar Sin. 

 

Ƙasar Sin ta ci gaba da rike matsayinta na babbar abokiyar hulɗar kasuwanci ta ASEAN tsawon shekaru 14 a jere, kuma ɓangarorin biyu sun kasance manyan abokan harkalla a fannin cinikayya mafi girma cikin shekaru uku a jere tun daga shekarar 2020. An kara inganta aikin gina yankin cinikayya maras shinge na ƙasar Sin da ASEAN, tare da ƙara ƙarfafa matsayin Sin da ASEAN a matsayin manyan abokan cinikayyar juna. A cikin ’yan shekarun nan, ƙasar Sin ta zama muhimmiyar ƙasa mai saka hannun jari a ƙasashen waje ga ƙasashen ASEAN.

ADVERTISEMENT
  • An Bude Taron Wakilai Na 8 Na Gamayyar Kungiyar Masu Bukata Ta Musamman Ta Sin

An ci gajiyar bikin baje koli na ƙasar Sin da ASEAN da kuma taron kolin harkokin kasuwanci, haɗin gwiwar tattalin arziki tsakanin ƙasashen ASEAN da ƙasar Sin sun haɓaka daga ingantacciyar cinikayya da zuba jari zuwa haɗin gwiwar ƙarfin samar da kayayyaki na ƙasa da ƙasa, da harkokin kuɗi, da tattalin arziki na fasahar zamani ko dijital, da kiwon lafiya, da yawon buɗe ido, da ilimi da dai sauransu. Haɗin gwiwar dake tsakanin ɓangarorin biyu na da matuƙar tasiri.

 

LABARAI MASU NASABA

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

Baje kolin ya ba da dama ga kasashen ASEAN don faɗaɗa fitar da kayayyaki masu inganci da fa’ida zuwa ƙasar Sin, da faɗaɗa cinikayya ta hanyar buɗe sabbin kasuwanni. Kana, zai taimaka wajen ba da gudummawa ga daidaiton ci gaban cinikayya tsakanin Sin da ASEAN.

 

Baje kolin bana ya zama wani abin ƙarfafa gwiwa ga gina yankin cinikayya maras shinge na Sin da ASEAN (FTA). A bukukuwan baje koli na ƙasar Sin da ASEAN na shekarun da suka gabata, an kiyasta cewa ‘yan kasuwa fiye da miliyan 1.1 ne suka halarci bukukuwan baje kolin a jimlance. Ana sa ran baje kolin bana wanda shi ne karo na 20 zai samu halartar ƙasashe fiye da 40 da kuma masu baje koli kusan 1,700.

 

Ga ƙasashen ASEAN, bikin baje kolin wani muhimmin al’amari ne na bunƙasa harkokin cinikayya, zuba jari, da musayar kayayyaki da yawon buɗe ido, wanda zai taimaka wajen ƙarfafa hulɗar tattalin arziki da cinikayya tsakanin ƙasashen Asiya da Sin da sauran ƙasashen yankin, da ƙara yin la’akari da damar da aka samu da aiwatar da yankin cinikayya maras shinge na ƙasar Sin da ASEAN.

 

A bana, masu baje koli kusan 640 daga ƙasashen ASEAN za su baje kolin hajojinsu da suka hada da biscuits, kofi, koko da cakulan da aka yi a ASEAN, da ruwan ‘ya’yan itace ko lemo, da kayan marmari da sauran abinci na musamman. kaza lika, za a yi nune-nunen tufafin sakawa, kayan ado irin su sarka, awarwaro, da ababe masu inganta lafiya da kyawun jiki, da sauran kayayyaki na musamman daga ƙasashen ASEAN.

 

Kamfanoni 120 na Vietnam za su baje kolin kayayyakin gona, da kayan ruwa, da abinci da aka sarrafa, da kayayyakin amfanin gida, yadi da tufafi, da kayayyakin ƙawata gida da aka kera da katako kaman kujeru da gadaje da dai sauransu. Kamfanonin Singapore 23 ne za su halarci baje kolin kuma za su gudanar da ayyukan zuba jari da ci gaban kasuwanci sama da 70.

 

A gefen bikin baje kolin, za a gudanar da taron baje kolin hadin gwiwar zuba jari, da taron zuba jari na masana’antu na ASEAN, da taron daidaita ayyuka, wani taron musamman kan zuba hannun jari a Sin wato “Invest in China Year–Enter Guangxi” a Turance, da dai sauransu, wadannan tarukan za su gudana ne don zurfafa hadin gwiwar tattalin arziki, cinikayya da zuba jari tsakanin Sin da ƙasashen ASEAN. (Yahaya)

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam
Daga Birnin Sin

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

November 11, 2025
Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa
Daga Birnin Sin

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

November 11, 2025
CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya
Daga Birnin Sin

CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya

November 11, 2025
Next Post

Babu Adawa Tsakanina Da Messi - Cewar Ronaldo

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 Tare Da Sace Babur A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 Tare Da Sace Babur A Nasarawa

November 12, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

November 12, 2025
Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

November 12, 2025
Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa

Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa

November 12, 2025
Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

Yadda Ɓarawo Ya Shiga Gidan Gwamnatin Kano Ya Saci Motar Ayarin Mataimakin Gwamna

November 12, 2025
Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

Zargin Kisan Kiristoci: Dalilan Da Ya Sa Trump Ba Zai Iya Kai Wa Nijeriya Hari Ba

November 12, 2025
Coas

Bayan Ganawa Da Tinubu, COAS Ya Tabbatar Wa ‘Yan Nijeriya Samun Ingantaccen Tsaro

November 11, 2025
Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam

November 11, 2025
Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

Bikin CIIE Ya Nuna Yadda Sin Ke Ba Da Jagora Kan Harkokin Bude Kofa

November 11, 2025
Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

Za Mu Ci Gaba Da Tallafa Wa ’Yansanda Domin Inganta Ayyukan Su A Zamfara – Gwamna Lawal

November 11, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.