ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babu Adawa Tsakanina Da Messi – Cewar Ronaldo

by Abba Ibrahim Wada
3 years ago

Dan wasa Cristiano Ronaldo ya bayyana cewa daga yanzu babu sauran adawa tsakaninsa da babban abokin hamayyarsa a fagen kwallon kafa, wato Lionel Messi, inda a cewarsa sun sauya tarihin kwallon kafar duniya. Ronaldo da Messi, ‘yan wasa biyu ne da ake yi wa lakabi da, ‘yan wasan da suka fi shahara a tarihi, wato ‘Gaot’ – sun sha fuskantar juna a lokacin da suke buga gasar La Liga a kungiyoyin Real Madrid da Barcelona.

Dan wasa Ronaldo ya ce dukkannin su ana girmama su a duniya, wannan shi ne babban abu mafi muhimmanci saboda haka lokaci ya yi da adawa a tsakanin su za ta zo karshe.
Ronaldo wanda ya lashe kyautar Ballon d’Or har sau biyar – a bana baya cikin mutanen da ke takarar kyautar karon farko tun shekara ta 2003, yayin da Messi zai iya lashe kyautar karo takwas a tarihi.

  • Ronaldo, Neymar Da Benzema Na Fatan Lashe Gasar Zakarun Asia

“Ya kafa tarihi, ni ma na kafa nawa, ya yi abin da ya dace, daga abin da na gani,” in ji Ronaldo mai shekara 38 a duniya wanda a yanzu yake buga wasa a kungiyar Al-Nassr ta Saudiyya.

ADVERTISEMENT

Dan kasar Portugal din ya ci gaba da cewa “bai kamata wadanda ke son Ronaldo, su ki Messi ba kuma a yanzu adawa ta kare, sun shafe shekara 15 suna jan zare a harkar kwallon kafa, don haka yanzu sun wuce abokai, sun zaman kwararrun abokan sana’a, kuma suna girmama junansu”.

‘Yan wasan sun cimma nasarori masu yawa a fagen wasan kwallon kafa, inda suka lashe kyaututtuka masu dimbin yawa a harkar kwallon kafa a matakin kungiyoyi da kasashe.

LABARAI MASU NASABA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

Ronaldo shi ne dan wasan da ya fi kowa zira kwallaye a Real Madrid inda ya ci 451 a wasa 438 da ya yi wa kungiyar, tare da cin kofuna 16 ciki har da Kofin Champions Leagues hudu da na La Liga biyu da na Copa del Rey biyu a tsowan shekara tara da ya yi a Real Madrid.

Shi kuwa Messi – wanda a yanzu ke wasa a kungiyar Inter Miami ta Amurka – ya kasance dan wasan da ya fi ci wa Barcelona kwallaye inda ya ci 674 a wasa 781 da ya buga wa kungiyar.

Messi – mai shekara 36 ya lashe kofuna 35 a Barcelona, ciki har da kofin La Liga 10 da kofin Champions League hudu da Copa del Rey bakwai a iya zaman da ya yi a kungiyar ta kasar Spaniya.

A matakin kasa kuwa Messi ya taimaka wa Argentina lashe Kofin Duniya da aka buga a Katar a 2022, sannan ya dauki kofin Copa America, yayin da shi kuma Ronaldo ya taimaka wa Portugal daukar kofin nahiyar Turai da kofin ‘Nations League’.

‘Yan wasan sun fuskanci juna a fili sau 36, haduwarsu ta karshe shi ne a watan Janairu a lokacin da kungiyar Messi ta PSG ta doke ta Al-Nassr da ci 5-4 a wasan sada zumunta.

Ronaldo
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Ka San Dalilin Da Ya Sa Chana Da Indiya Ba Sa Buga Kofin Duniya?
  • Abba Ibrahim Wada
    Gwamnatin Kaduna Ta Yaba Wa NSA Kan Shirin Samar Da Dakarun Tsaron Daji
  • Abba Ibrahim Wada
    Lampard Zai Ci Gaba Da Zama A Coventry City

MASU ALAKA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
Wasanni

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
Wasanni

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Wasanni

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026
Next Post
Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa Ya Zama Dole

Ci Gaban Kasashe Masu Tasowa Ya Zama Dole

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.