• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Daɗe Ana Yi Sai Gaskiya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
A Daɗe Ana Yi Sai Gaskiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shekarar 2023 ta cika shekaru 20 da kulla dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare tsakanin Sin da ƙungiyar ASEAN wato ƙungiyar ƙasashen kudu maso gabashin Asiya, da kuma cika shekaru 20 da kafuwar baje kolin Sin da ASEAN. Wannan ya ba da muhimmiyar ma’ana ga bikin baje kolin Sin da ASEAN na bana, wanda aka bude a ranar 17 ga watan Satumba a birnin Nanning na jihar Guangxi ta kabilar Zhuang mai cin gashin kanta ta kudancin ƙasar Sin. 

 

Ƙasar Sin ta ci gaba da rike matsayinta na babbar abokiyar hulɗar kasuwanci ta ASEAN tsawon shekaru 14 a jere, kuma ɓangarorin biyu sun kasance manyan abokan harkalla a fannin cinikayya mafi girma cikin shekaru uku a jere tun daga shekarar 2020. An kara inganta aikin gina yankin cinikayya maras shinge na ƙasar Sin da ASEAN, tare da ƙara ƙarfafa matsayin Sin da ASEAN a matsayin manyan abokan cinikayyar juna. A cikin ’yan shekarun nan, ƙasar Sin ta zama muhimmiyar ƙasa mai saka hannun jari a ƙasashen waje ga ƙasashen ASEAN.

  • An Bude Taron Wakilai Na 8 Na Gamayyar Kungiyar Masu Bukata Ta Musamman Ta Sin

An ci gajiyar bikin baje koli na ƙasar Sin da ASEAN da kuma taron kolin harkokin kasuwanci, haɗin gwiwar tattalin arziki tsakanin ƙasashen ASEAN da ƙasar Sin sun haɓaka daga ingantacciyar cinikayya da zuba jari zuwa haɗin gwiwar ƙarfin samar da kayayyaki na ƙasa da ƙasa, da harkokin kuɗi, da tattalin arziki na fasahar zamani ko dijital, da kiwon lafiya, da yawon buɗe ido, da ilimi da dai sauransu. Haɗin gwiwar dake tsakanin ɓangarorin biyu na da matuƙar tasiri.

 

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

Baje kolin ya ba da dama ga kasashen ASEAN don faɗaɗa fitar da kayayyaki masu inganci da fa’ida zuwa ƙasar Sin, da faɗaɗa cinikayya ta hanyar buɗe sabbin kasuwanni. Kana, zai taimaka wajen ba da gudummawa ga daidaiton ci gaban cinikayya tsakanin Sin da ASEAN.

 

Baje kolin bana ya zama wani abin ƙarfafa gwiwa ga gina yankin cinikayya maras shinge na Sin da ASEAN (FTA). A bukukuwan baje koli na ƙasar Sin da ASEAN na shekarun da suka gabata, an kiyasta cewa ‘yan kasuwa fiye da miliyan 1.1 ne suka halarci bukukuwan baje kolin a jimlance. Ana sa ran baje kolin bana wanda shi ne karo na 20 zai samu halartar ƙasashe fiye da 40 da kuma masu baje koli kusan 1,700.

 

Ga ƙasashen ASEAN, bikin baje kolin wani muhimmin al’amari ne na bunƙasa harkokin cinikayya, zuba jari, da musayar kayayyaki da yawon buɗe ido, wanda zai taimaka wajen ƙarfafa hulɗar tattalin arziki da cinikayya tsakanin ƙasashen Asiya da Sin da sauran ƙasashen yankin, da ƙara yin la’akari da damar da aka samu da aiwatar da yankin cinikayya maras shinge na ƙasar Sin da ASEAN.

 

A bana, masu baje koli kusan 640 daga ƙasashen ASEAN za su baje kolin hajojinsu da suka hada da biscuits, kofi, koko da cakulan da aka yi a ASEAN, da ruwan ‘ya’yan itace ko lemo, da kayan marmari da sauran abinci na musamman. kaza lika, za a yi nune-nunen tufafin sakawa, kayan ado irin su sarka, awarwaro, da ababe masu inganta lafiya da kyawun jiki, da sauran kayayyaki na musamman daga ƙasashen ASEAN.

 

Kamfanoni 120 na Vietnam za su baje kolin kayayyakin gona, da kayan ruwa, da abinci da aka sarrafa, da kayayyakin amfanin gida, yadi da tufafi, da kayayyakin ƙawata gida da aka kera da katako kaman kujeru da gadaje da dai sauransu. Kamfanonin Singapore 23 ne za su halarci baje kolin kuma za su gudanar da ayyukan zuba jari da ci gaban kasuwanci sama da 70.

 

A gefen bikin baje kolin, za a gudanar da taron baje kolin hadin gwiwar zuba jari, da taron zuba jari na masana’antu na ASEAN, da taron daidaita ayyuka, wani taron musamman kan zuba hannun jari a Sin wato “Invest in China Year–Enter Guangxi” a Turance, da dai sauransu, wadannan tarukan za su gudana ne don zurfafa hadin gwiwar tattalin arziki, cinikayya da zuba jari tsakanin Sin da ƙasashen ASEAN. (Yahaya)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Sanya Tsofaffin Gandun Daji Na Shayi Dake Pu’er Na Sin A Cikin Jerin Wuraren Tarihi Na Duniya

Next Post

Babu Adawa Tsakanina Da Messi – Cewar Ronaldo

Related

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

9 hours ago
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi
Daga Birnin Sin

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

10 hours ago
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

10 hours ago
Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya
Daga Birnin Sin

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

11 hours ago
Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

13 hours ago
An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya
Daga Birnin Sin

An Watsa Shirin Talabijin Mai Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” A Italiya

15 hours ago
Next Post

Babu Adawa Tsakanina Da Messi - Cewar Ronaldo

LABARAI MASU NASABA

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

June 27, 2025
Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

June 27, 2025
Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

June 27, 2025
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

June 26, 2025
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

June 26, 2025
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

June 26, 2025
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

June 26, 2025
Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

June 26, 2025
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

June 26, 2025
Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.