• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Gwabza Fada Ko A Rungumi Zaman Lafiya?

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
A Gwabza Fada Ko A Rungumi Zaman Lafiya?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan nan, bisa sulhun da kasar Sin ta yi, kasashen Saudiyya da Iran sun farfado da huldarsu bayan da suka katse huldar jakadanci na tsawon shekaru bakwai, lamarin da ya bude sabon babin dangantakar kasashen biyu, baya ga yadda hakan ya haskaka duniyarmu da ta shiga duhu sakamakon matsalar Ukraine.

Yadda Saudiyya da Iran suka farfado da huldarsu abu ne mai ma’ana ga kasashen biyu, baya ga haka, yana kuma da muhimmanci ga sauran kasashen duniya. Na farko, lamarin ya shaida mana cewa, kasa da kasa na iya zama lafiya da juna da tabbatar da cin moriyar juna bisa tushen martaba juna. Na biyu kuma, ya haifar da wani yanayi na rungumar zaman lafiya a shiyyoyin gabas ta tsakiya da arewacin nahiyar Afirka da suka dade suna fuskantar tashin hankali, har ma da duniya baki daya.

  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran: Kasar Sin Ta Taimaka Wajen Shimfida Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali A Gabas Ta Tsakiya

In mun waiwayi baya, za mu fahimci cewa, Amurka da sauran kasashen yamma ne suka yi ta tada rikici da jawo rarrabuwar kawuna a tsakanin kasashen gabas ta tsakiya da arewacin nahiyar Afirka, kuma kasancewar Saudiyya da Iran manyan kasashen shiyyar, sun tabka mummunan hasara sanadiyar hakan,har daga baya suka gane halin kasar Amurka tare da fahimtar cewa, ta hanyar yin shawarwari da juna ne kawai za su iya fita daga mawuyacin halin.

Matsalar Ukraine da aka shafe sama da shekara guda ana fama da ita, ita ta hannun Amurka, kuma har yanzu Amurka na kokarin rura wutar rikicin. A ranar 20 ga wata, sakataren harkokin wajen kasar Amurka Antony Blinken ya bayyana cewa, kasarsa za ta kara samar da gudummawar soji da darajarta ta kai dalar Amurka miliyan 35 ga Ukraine. Alkaluma sun shaida cewa, ya zuwa tsakiyar watan Janairun bana, gaba daya Amurka ta samar da gudummawar soja da ta kai dala biliyan 46.6 ga kasar Ukraine, adadin da har ya wuce matsakaicin kudin da ta ware ga yakin Afghanistan a kowace shekara. Kwatankwacin abubuwan da Amurka ta aikata, a cikin shekara sama da daya tun bayan aukuwar rikicin Ukraine, kasar Sin ba ta taba tsayawa tana kallon rikicin ba, ballantana ta rura wutar rikicin, a maimakon haka kuma, ta yi ta kokarin gano bakin zaren warware shi. Idan ba mu manta ba, a ranar 24 ga watan Faburairun da ya wuce, kasar Sin ta fitar da takardar da ke bayani kan matsayinta a kan warware matsalar Ukraine a siyasance, inda ta samar da dabararta a wani kokari na daidaita matsalar a siyasance.

A hakika irin bambancin matakan da kasashen Sin da Amurka suka dauka ya faru ne sakamakon bambancin da suka samu ta fannin fahimtar tsaron kasa da kuma cudanyar kasa da kasa. Misali a game da tsaron kasar, kasar Sin na dora muhimmanci a kan tsaron kanta da ma na sauran kasashen duniya baki daya, don gina al’ummar duniya mai kyakkyawar makoma ta bai daya, a yayin da Amurka ke nuna son kai wajen kiyaye tsaron kanta, kuma tana daukar barazanar da moriyarta ke fuskanta a kowane bangaren duniya a matsayin abin da zai illata tsaronta. A game da cudanyar kasa da kasa kuma, manufar kasar Sin ita ce zama lafiya da juna tare da martaba bambancin juna ta fannoni daban daban, a yayin da Amurka ke ganin duk wadda ke da bambancin ra’ayi da ita ba za ta taba zama abokiyarta ba, sai ma ta zama abokiyar gabanta.

Labarai Masu Nasaba

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Kasancewarsu a duniya guda, makomar dan Adam ma daya ce. A cikin ‘yan shekarun baya, kasar Sin ta gabatar da shawarar raya duniya da shawarar kiyaye tsaron duniya da ma shawarar raya wayewar kan duniya, a wani kokari na tabbatar da dauwamammen zaman lafiya a duniya, ta yadda kowace kasa za ta kasance cikin yanayi na zaman lafiya da kwanciyar hankali, kuma kowace kasa za ta samu hakkin tabbatar da ci gabanta, kuma al’ummar kasa da kasa za su ji dadin zaman rayuwarsu. A ganina, wannan shawarar da kasar Sin ta gabatar, ta kuma kasance buri na bai daya na al’ummar duniya.(Mai Zane:Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin: Wajibi Ne Kasa Da Kasa Su Taimakawa Nahiyar Afrika Yakar Ta’addanci

Next Post

Yansanda Sun Cafke Masu Garkuwa 2 Bayan Musayar Wuta A Jihar Ogun

Related

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

3 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

5 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

5 hours ago
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

22 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

22 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

1 day ago
Next Post
Yansanda Sun Cafke  Masu Garkuwa 2 Bayan Musayar Wuta A Jihar Ogun

Yansanda Sun Cafke Masu Garkuwa 2 Bayan Musayar Wuta A Jihar Ogun

LABARAI MASU NASABA

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
lafiya

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.