• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Gwabza Fada Ko A Rungumi Zaman Lafiya?

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
A Gwabza Fada Ko A Rungumi Zaman Lafiya?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwanan nan, bisa sulhun da kasar Sin ta yi, kasashen Saudiyya da Iran sun farfado da huldarsu bayan da suka katse huldar jakadanci na tsawon shekaru bakwai, lamarin da ya bude sabon babin dangantakar kasashen biyu, baya ga yadda hakan ya haskaka duniyarmu da ta shiga duhu sakamakon matsalar Ukraine.

Yadda Saudiyya da Iran suka farfado da huldarsu abu ne mai ma’ana ga kasashen biyu, baya ga haka, yana kuma da muhimmanci ga sauran kasashen duniya. Na farko, lamarin ya shaida mana cewa, kasa da kasa na iya zama lafiya da juna da tabbatar da cin moriyar juna bisa tushen martaba juna. Na biyu kuma, ya haifar da wani yanayi na rungumar zaman lafiya a shiyyoyin gabas ta tsakiya da arewacin nahiyar Afirka da suka dade suna fuskantar tashin hankali, har ma da duniya baki daya.

  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran: Kasar Sin Ta Taimaka Wajen Shimfida Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali A Gabas Ta Tsakiya

In mun waiwayi baya, za mu fahimci cewa, Amurka da sauran kasashen yamma ne suka yi ta tada rikici da jawo rarrabuwar kawuna a tsakanin kasashen gabas ta tsakiya da arewacin nahiyar Afirka, kuma kasancewar Saudiyya da Iran manyan kasashen shiyyar, sun tabka mummunan hasara sanadiyar hakan,har daga baya suka gane halin kasar Amurka tare da fahimtar cewa, ta hanyar yin shawarwari da juna ne kawai za su iya fita daga mawuyacin halin.

Matsalar Ukraine da aka shafe sama da shekara guda ana fama da ita, ita ta hannun Amurka, kuma har yanzu Amurka na kokarin rura wutar rikicin. A ranar 20 ga wata, sakataren harkokin wajen kasar Amurka Antony Blinken ya bayyana cewa, kasarsa za ta kara samar da gudummawar soji da darajarta ta kai dalar Amurka miliyan 35 ga Ukraine. Alkaluma sun shaida cewa, ya zuwa tsakiyar watan Janairun bana, gaba daya Amurka ta samar da gudummawar soja da ta kai dala biliyan 46.6 ga kasar Ukraine, adadin da har ya wuce matsakaicin kudin da ta ware ga yakin Afghanistan a kowace shekara. Kwatankwacin abubuwan da Amurka ta aikata, a cikin shekara sama da daya tun bayan aukuwar rikicin Ukraine, kasar Sin ba ta taba tsayawa tana kallon rikicin ba, ballantana ta rura wutar rikicin, a maimakon haka kuma, ta yi ta kokarin gano bakin zaren warware shi. Idan ba mu manta ba, a ranar 24 ga watan Faburairun da ya wuce, kasar Sin ta fitar da takardar da ke bayani kan matsayinta a kan warware matsalar Ukraine a siyasance, inda ta samar da dabararta a wani kokari na daidaita matsalar a siyasance.

A hakika irin bambancin matakan da kasashen Sin da Amurka suka dauka ya faru ne sakamakon bambancin da suka samu ta fannin fahimtar tsaron kasa da kuma cudanyar kasa da kasa. Misali a game da tsaron kasar, kasar Sin na dora muhimmanci a kan tsaron kanta da ma na sauran kasashen duniya baki daya, don gina al’ummar duniya mai kyakkyawar makoma ta bai daya, a yayin da Amurka ke nuna son kai wajen kiyaye tsaron kanta, kuma tana daukar barazanar da moriyarta ke fuskanta a kowane bangaren duniya a matsayin abin da zai illata tsaronta. A game da cudanyar kasa da kasa kuma, manufar kasar Sin ita ce zama lafiya da juna tare da martaba bambancin juna ta fannoni daban daban, a yayin da Amurka ke ganin duk wadda ke da bambancin ra’ayi da ita ba za ta taba zama abokiyarta ba, sai ma ta zama abokiyar gabanta.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Kasancewarsu a duniya guda, makomar dan Adam ma daya ce. A cikin ‘yan shekarun baya, kasar Sin ta gabatar da shawarar raya duniya da shawarar kiyaye tsaron duniya da ma shawarar raya wayewar kan duniya, a wani kokari na tabbatar da dauwamammen zaman lafiya a duniya, ta yadda kowace kasa za ta kasance cikin yanayi na zaman lafiya da kwanciyar hankali, kuma kowace kasa za ta samu hakkin tabbatar da ci gabanta, kuma al’ummar kasa da kasa za su ji dadin zaman rayuwarsu. A ganina, wannan shawarar da kasar Sin ta gabatar, ta kuma kasance buri na bai daya na al’ummar duniya.(Mai Zane:Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin: Wajibi Ne Kasa Da Kasa Su Taimakawa Nahiyar Afrika Yakar Ta’addanci

Next Post

Yansanda Sun Cafke Masu Garkuwa 2 Bayan Musayar Wuta A Jihar Ogun

Related

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar
Daga Birnin Sin

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

14 hours ago
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta
Daga Birnin Sin

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

15 hours ago
Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila
Daga Birnin Sin

Xi Ya Yi Kira Ga Mazauna Wani Kauye Dake Xizang Da Su Rike ‘Yan Uwantakar Kabila

17 hours ago
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

1 day ago
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

2 days ago
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

2 days ago
Next Post
Yansanda Sun Cafke  Masu Garkuwa 2 Bayan Musayar Wuta A Jihar Ogun

Yansanda Sun Cafke Masu Garkuwa 2 Bayan Musayar Wuta A Jihar Ogun

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina

June 30, 2025
Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

Sojoji Sun Kashe Shugaban Ƴan Ta’adda Mai Dada

June 29, 2025
Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

Sharrin Ƴan Adawa Ne, Gwamnati Ta Ƙaryata Labarin Cire SGF Akume 

June 29, 2025
An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari

June 29, 2025
Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

Babbar Mota Ta Afka Cikin Kasuwa A Taraba, Mutane Da Yawa Sun Mutu

June 29, 2025
Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

Shugaban Majalisar Dokokin Jama’ar Kasar Mexico: Tunanin Raya Al’umma Mai Kyakkyawar Makoma Ga Dukkan Bil’adama Da Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Ya Kayatar

June 29, 2025
Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

Sin Na Adawa Da Duk Wata Yarjejeniyar Haraji Da Ka Iya Illata Moriyarta

June 29, 2025
2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

2027: Ƴan Adawa Na Ƙara Ƙaimin Kawar Da Tinubu

June 29, 2025
Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

Yadda Yaƙin Iran Da Isra’ila Zai Iya Shafar Zamantakewa Da Tattalin Arziƙin Nijeriya

June 29, 2025
Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa

June 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.