ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Gwabza Fada Ko A Rungumi Zaman Lafiya?

by CMG Hausa
3 years ago
lafiya

Kwanan nan, bisa sulhun da kasar Sin ta yi, kasashen Saudiyya da Iran sun farfado da huldarsu bayan da suka katse huldar jakadanci na tsawon shekaru bakwai, lamarin da ya bude sabon babin dangantakar kasashen biyu, baya ga yadda hakan ya haskaka duniyarmu da ta shiga duhu sakamakon matsalar Ukraine.

Yadda Saudiyya da Iran suka farfado da huldarsu abu ne mai ma’ana ga kasashen biyu, baya ga haka, yana kuma da muhimmanci ga sauran kasashen duniya. Na farko, lamarin ya shaida mana cewa, kasa da kasa na iya zama lafiya da juna da tabbatar da cin moriyar juna bisa tushen martaba juna. Na biyu kuma, ya haifar da wani yanayi na rungumar zaman lafiya a shiyyoyin gabas ta tsakiya da arewacin nahiyar Afirka da suka dade suna fuskantar tashin hankali, har ma da duniya baki daya.

  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran: Kasar Sin Ta Taimaka Wajen Shimfida Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali A Gabas Ta Tsakiya

In mun waiwayi baya, za mu fahimci cewa, Amurka da sauran kasashen yamma ne suka yi ta tada rikici da jawo rarrabuwar kawuna a tsakanin kasashen gabas ta tsakiya da arewacin nahiyar Afirka, kuma kasancewar Saudiyya da Iran manyan kasashen shiyyar, sun tabka mummunan hasara sanadiyar hakan,har daga baya suka gane halin kasar Amurka tare da fahimtar cewa, ta hanyar yin shawarwari da juna ne kawai za su iya fita daga mawuyacin halin.

ADVERTISEMENT

Matsalar Ukraine da aka shafe sama da shekara guda ana fama da ita, ita ta hannun Amurka, kuma har yanzu Amurka na kokarin rura wutar rikicin. A ranar 20 ga wata, sakataren harkokin wajen kasar Amurka Antony Blinken ya bayyana cewa, kasarsa za ta kara samar da gudummawar soji da darajarta ta kai dalar Amurka miliyan 35 ga Ukraine. Alkaluma sun shaida cewa, ya zuwa tsakiyar watan Janairun bana, gaba daya Amurka ta samar da gudummawar soja da ta kai dala biliyan 46.6 ga kasar Ukraine, adadin da har ya wuce matsakaicin kudin da ta ware ga yakin Afghanistan a kowace shekara. Kwatankwacin abubuwan da Amurka ta aikata, a cikin shekara sama da daya tun bayan aukuwar rikicin Ukraine, kasar Sin ba ta taba tsayawa tana kallon rikicin ba, ballantana ta rura wutar rikicin, a maimakon haka kuma, ta yi ta kokarin gano bakin zaren warware shi. Idan ba mu manta ba, a ranar 24 ga watan Faburairun da ya wuce, kasar Sin ta fitar da takardar da ke bayani kan matsayinta a kan warware matsalar Ukraine a siyasance, inda ta samar da dabararta a wani kokari na daidaita matsalar a siyasance.

A hakika irin bambancin matakan da kasashen Sin da Amurka suka dauka ya faru ne sakamakon bambancin da suka samu ta fannin fahimtar tsaron kasa da kuma cudanyar kasa da kasa. Misali a game da tsaron kasar, kasar Sin na dora muhimmanci a kan tsaron kanta da ma na sauran kasashen duniya baki daya, don gina al’ummar duniya mai kyakkyawar makoma ta bai daya, a yayin da Amurka ke nuna son kai wajen kiyaye tsaron kanta, kuma tana daukar barazanar da moriyarta ke fuskanta a kowane bangaren duniya a matsayin abin da zai illata tsaronta. A game da cudanyar kasa da kasa kuma, manufar kasar Sin ita ce zama lafiya da juna tare da martaba bambancin juna ta fannoni daban daban, a yayin da Amurka ke ganin duk wadda ke da bambancin ra’ayi da ita ba za ta taba zama abokiyarta ba, sai ma ta zama abokiyar gabanta.

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Kasancewarsu a duniya guda, makomar dan Adam ma daya ce. A cikin ‘yan shekarun baya, kasar Sin ta gabatar da shawarar raya duniya da shawarar kiyaye tsaron duniya da ma shawarar raya wayewar kan duniya, a wani kokari na tabbatar da dauwamammen zaman lafiya a duniya, ta yadda kowace kasa za ta kasance cikin yanayi na zaman lafiya da kwanciyar hankali, kuma kowace kasa za ta samu hakkin tabbatar da ci gabanta, kuma al’ummar kasa da kasa za su ji dadin zaman rayuwarsu. A ganina, wannan shawarar da kasar Sin ta gabatar, ta kuma kasance buri na bai daya na al’ummar duniya.(Mai Zane:Mustapha Bulama)

lafiya
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Daga Birnin Sin

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Next Post
Yansanda Sun Cafke  Masu Garkuwa 2 Bayan Musayar Wuta A Jihar Ogun

Yansanda Sun Cafke Masu Garkuwa 2 Bayan Musayar Wuta A Jihar Ogun

LABARAI MASU NASABA

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

Ra’yin Sin Da Afirka Ya Zo Daya A Fannin Fasahar AI

July 16, 2026
Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

Duk Da Sauye-Sauyen Tattalin Arziƙi Kashi 79% Na Ƴan Nijeriya Na Cikin Talauci – Bankin Duniya

July 16, 2026
M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.