• English
  • Business News
Tuesday, July 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Hada Kai Domin Yaki Da Shan Miyagun Kwayoyi (Ra’ayinmu)

by Sulaiman
3 years ago
in Bakon Marubuci
0
A Hada Kai Domin Yaki Da Shan Miyagun Kwayoyi (Ra’ayinmu)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar 26 ga watan Yuni na kowacce shekara ne Majalisar Dinkin Duniya ta ware domin fadakar da al’umma a kan barnar da shaye-shayen miyagun kwayoyi ke yi ga rayuwar al’umma musamman matasa, barna ya munana, ta haka ake saran al’umma za su fahimci barnar da matsalar da ke tattare da nomawa da safarar muggan kwayoyi a cikin al’umma.

Abin takaici shi ne wannan gangamin na wannan shekarar yana zuwa ne a daidai lokacin da mu’amala da kwayoyi a tsakanin matasanmu take dada karuwa ne a kullum. Kidididgar da aka yi a shekarar 2019, ta nuna cewa, an fi shan tabar wiwi a tsakanin matasan inda aka gano cewa, akalla ‘yan Nijeriya fiye da Miliyan 10.6 ke shan tabar wiwi, inda wasu na fara shan tabar ne tun suna shekara 19 a duniya.

  • NDLEA Ta Damke Wata Mata Za Ta Yi Safarar Miyagun Kwayoyi Zuwa Oman

Haka kuma binciken wanda kungiyar ‘Global Drug Surbey’ ta gudanar ya nuna cewa, an fi shan kwayar ne a yankin Afrika ta Yamma.

Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta tabbatar da cewa, tabar wiwi ce aka fi sha a yankin Afirka, inda aka samu kashi 5.2 zuwa 13.5 na masu shan tabar a yankin Afirka mafi yawansu kuma na yankin Afirka ta Yanma ne, ana kuma iya cewa, al’amarin kwayoyin ya yi kamari a Nijeriya fiye da wata kasa a Afirka.

Haka kuma a binciken da kungiyar ‘National Drug Use and Health Surbey’ ta gudanar a shekarar 2018, ta gano cewa, fiye da mutum 376,000 na cikin tsananin mu’amala da kwayoyi, inda daya daga cikin mutum 5 zaka samu daya yana amfani da kwayoyi da ake tsira wa da allura. Fiye da mutum 80,000 da ke amfani da allurar wajen zukar kwayoyin na fuskantar yada cututtuka kamar su Kanjamar da cutar hanta.

Labarai Masu Nasaba

Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus

Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 

Babu kokwanto, nada Birgediya Janar Buba Marwa a mastayin shugaban Hukumar Yaki da Safarar Miyagun Kwayoyi ya taimaka kwarai wajen zaburar da hukumar a yakin da ake yi da safarar miyagun kwayoyi a Nijeriya.

Yana da muhimmanci a fahimci cewa a cikin wata 17 da suka wuce an samu nasarar kama masu safarar miyagun kwayoyi fiye da 17, 647 an kuma samu nasarar garkame manyan diloli masu safara kwayoyin 10, haka nan kuma hukumar ta samu nasarar zartar da hukunci a kan mutum 2,369 an kuma samu nasarar warkar da masu mu’amala da miyagun kwayoyin fiye 11,000 a daidai wanna lokacin da ake magana.

Ra’ayin wannan jaridar shi ne, ya zama dole a yi nasara a yakin da ake fuskanta a kan safara da amfani da miyagun kwayoyi saboda dangantakar miyagun kwayoyi da matsalar tsaro.

Idan za a iya tunawa a shekarar 2020, mai ba shugaban kasa shawara a kan harkar tsaro, Manjo Janar Babagana Monguno (mai ritaya) ya danganta yawaitar matsalar a kasar nan da yadda ake mu’amala da miyagun kwayoyi, ya kuma ce, lallai abin ya zama abin tayar da hankali.

A halin yanzu an dora Nijeriya a matsayin kasar da ta fi hatsari a kan ayyukan ‘yan ta’adda. A bin takaicin shi ne yadda harkokin ‘yan ta’adda ke kara karuwa a kullum suna cin karen su babu babbaka, duk da cewa, babu wani shashe na duniya da ya tsira daga abubuwan da suka shafi ayyukan ‘yan ta’adda amma lamarin Nijeriya yana da ban tsoro.

Don nuna jajircewarsa a kan yaki da miyagun kwayoyi, shugaban kasa Muhammadu Buhari, a shekarar da ta gabata ya kaddamar da shiri na musamman da aka yi wa lakabi da ‘War Against Drug Abuse” (WADA)’ da kuma kundi na musanmman mai suna “National Drug Control Master Plan 2021-2025” na yadda za a fuskanci yaki da miyagun kwayoyi a sasan kasar nan.

Shugaban kasar ya kuma ce, barazanar da miyagun kwayo ke yi wa kasar nan ya fi na ayyukan ta’addanci da ake fuskanta.
Mun amince da bayanin shugaban kasa na cewa, miyagun kwayoyi ya taimaka wajen kara zafafa ayyukan masu garkuwa da mutane da ‘yan ta’adda a sassan Nijeriya, mun kuma amince da irin nasarorin da NDLEA ke samu a yaki da miyagun kwayoyi, muna kuma kira da a kara kaimi wajen zafafa yakin da ake yi da masu safara da mu’amala da miyagun kwayoyi a sassan kasar nan ta haka za a tabbatar da rage lamarin yadda ya kamata.

Wannan yaki na kowa da kowa ne a saboda haka muna kira ga iyalai, makarantu da kungiyoyi masu zaman kansu da sauran al’umma gaba daya su kawo nasu gudummawar don samun nasarar fatattakar masu safarar kwayoyi da masu mu’amala da ita, tare da kuma ba hukumar NDLEA goyon bayan da take bukata gaba daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Farashin Alkama Ya Sauka a Duniya

Next Post

2023: Jama’a Su Ajiye Jam’iyya Su Zabi Cancanta – Malam Murtala

Related

Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus
Bakon Marubuci

Yawaitar Al’umma: Martanin Karl Marx Ga Rabaran Malthus

4 days ago
Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 
Bakon Marubuci

Dabi’a: Yadda Ake Gini Da Rusa Ta 

3 weeks ago
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)
Bakon Marubuci

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (3)

1 month ago
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)
Bakon Marubuci

SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)

2 months ago
Ta Ya Ake Gudanar Da Nagartacciyar Rayuwa?
Bakon Marubuci

Ta Ya Ake Gudanar Da Nagartacciyar Rayuwa?

3 months ago
Waraka Daga Bashin Ketare
Bakon Marubuci

Waraka Daga Bashin Ketare

3 months ago
Next Post
2023: Jama’a Su Ajiye Jam’iyya Su Zabi Cancanta – Malam Murtala

2023: Jama'a Su Ajiye Jam'iyya Su Zabi Cancanta - Malam Murtala

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kuɓutar Da ‘Yan Ghana 19 Da Aka Yaudare Su Zuwa Nijeriya

July 8, 2025
ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

July 8, 2025
Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato

‘Yan Bindiga Sun Hallaka ‘Yan Sa-kai Sama Da 70 A Filato

July 8, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027

July 8, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

July 8, 2025
Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 7, 2025
Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

July 7, 2025
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

July 7, 2025
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

July 7, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

July 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.