ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Raya Al’ada: Bikin Kalankuwa Na 2025 A Kano

by Muktar Anwar
9 months ago
Kano

Wadanda suke da ilimi game da muhimmancin raya al’da, ko kusa, ba su yin kasa-a-gwiwa wajen raya ta, daga lokaci zuwa lokaci. Bugu da kari, batun “raya al’da”, wani abu ne da yake da fadi ainun, wanda ya kunshi duka wani janibi na rayuwar jama’ar gari, kasa, birni, kauye, wani lokaci ma na hade al’ummun nahiya guda, idan aka fadada ma’anar al’dar mutane.

Kamar yadda bayanai ke zuwa daga majiyoyi masu tushe daga tsagin gwamnatin Jihar Kano cewa, akwai wani gagarumin “Bikin Nuna Fasahohi da Al’adun Bahaushen Kano” da Hukumar Tarihi da Al’adu ta Kano ke kan shiryawa karkashin sahalewar mai girma gwamna, Abba K. Yusuf, wanda ake wa bikin take, ko ace lakabi da KANFES “KANFEST, 2025 – KANO FESTIBAL”. Masana da wasu daga masu sharhi a kan al’adar Malam Bahaushe a Kano, sun kalli wannan biki na nuna fasahar Bahaushe da al’adunsa da ake yunkurin gudanarwa a Jihar Kano a cikin wata mai kamawa na Okotoba, 2025, a matsayin wanda ba a taba shirya hatta kwatankwacinsa a Kanon ba. Sun kara da cewa, manyan bukukuwan raya al’dar Bahaushen Kano da ake shiryawa a garin, bai wuce hawan daushe ba. Wanda ya kunshi nuna kayan kawa na dawakai, sukuwa, kade-kade da sauransu.

  • Manyan Jami’an Kasashen Afirka Suna Fatan Fadada Hadin Gwiwa Da Kasar Sin
  • Jami’an Tsaro Sun Kashe Ƙasurgumin Mai Garkuwa Da Mutane, Maidawa Da Wasu A Kwara

Na’am, wasannin dambe, kokawa da sauran wasannin da ke da jibi da al’dar Bahaushe da ake gani nan da can a kwaryar birni ko a karkara a na shiryawa, gaba daya, ko a ce akasari, ba hukumomi ne ke shiryawa ba. Wannan gagarimin gangankon bikin raya al’adar Bahaushen Kano da ake kokarin shiryawa karkashin gwamnatin Abba Gida-Gida, babu shakka, wata gwamnati a Kano, ta Soja, ko ta Farar-hula, ba ta taba katarin shirya irin bikin ba. Kafin a je da nisa, ko akwai wani alfanu da ake girba karkashin raya al’ada?. Mece ce ma al’adar kanta?.

ADVERTISEMENT

A takaicen takaitawa, tsarin zamantakewar al’umma, tufafinsu, abincinsu, gine-ginensu, sana’o’insu, addininsu, halaiyarsu da sauransu, duka, sukan taru ne su fassara mutanen da suka yi tarayya cikin wadannan abubuwa da aka zayyano cewa, suna da al’ada iri kaza, ko iri guda. Da mutum zai binciki tarihin Malam Bahaushe, za a iske cewa, tun gabanin zuwan Turawan Ingilishi wannan kasa, yana da kyawawan al’adunsa, son kowa, kin wanda ya rasa. Bayan iya dasisa ta Bature, da kuma sakaci na Bahaushen, sune suka hadu, tare da mantar da Bahaushen al’adar tasa, alhali da yawa daga al’ummun Duniya, na kife ne bisa al’adunsu, wanda a sanadiyyar rikonsu da al’adun nasu ne, fannoni daban-daban na rayuwar yau da kullum, irin su bangaren tattalin arziki, shugabanci, masana’antu, sana’o’i da sauransu suke kan bunkasa nan da nan. Game da wannan batu, kasar Sin a yau, ta ishi mai karatu hujjar samun ci gaba a kowane fanni na rayuwar jama’a, wanda wannan kasa ta Sin ko Chana, na daga kasashen da Duniya ta shaide su, wajen yin riko da al’dar Kaka da Kakanni.

 

LABARAI MASU NASABA

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki

A Karshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Damar Yin Takara

Wasan Kalankuwa A Nijeriya, 1977

A gwamnatance a wannan kasa, an fara shirya manyan bukukuwan nuna fasahohinmu da aladunmu na-dauri, cikin Shekarar 1977 a Legas. Wanda aka fara gudanar da taron, daga 15 ga Watan Janairu, zuwa 12 ga Watan Farairun Shekarar 1977. A farkon lamari, an niyyaci ci gaba da shirya bikin na baje-kolin al’ada ne a duk Shekara, da niyyar samar da hadin-kai a tsakanin jama’ar Kasa bakidaya. Da farko an kira bikin ne da FESTAC ’77, daga baya aka koma kiransa da NAFEST (National Festibal of Arts and Culture).

Saboda muhimmancin irin wadannan bukukuwa, lokacin da aka fara shirya shi a wannan kasa, an sami mahalarta taron ne daga mabanbantan kasashe har kimanin hamsin da biyar (55). Ba ya ga yunkurin samun hadin-kai a tsakanin al’umar wannan kasa, an kara fadada kudirin taron har zuwa ga daukacin sassan duniya. Inda aka nuna cewa, duk wani mutum bakar-fata dake zaune a wannan nahiya tamu ta Afurka, da sauran kasashen Duniya, shi ma wannan taron nuna fasahohin mutane bakaen fata da al’adunsu nasa ne, a matsayinsa na guda daga jinsin bakar fata. Irin wannan wasan Kalankuwa na farko, zai iya tunawa mutumin wannan kasa, yawan kiraye-kirayen da marigayi Dr Yusuf Maitama Sule Danmasanin Kano ke yi cewa, lokaci ya yi da ya dace jama’ar Afurka su tashi su lalubo irin tsarin Dimukradiyyar da ta dace da mutanensu bakaken-fata, tare da rabuwa da irin dimukradiyyar kasashen Turai da Amurka.

 

Makasudin Shirya Wannan Biki A Kano, KANFEST, 2025

Da mutum zai tsaya ya dubi irin dalilan da masu shirya wannan taro a Kano suka gabatar, lalle zai kai ga fahimtar yiwuwar ciyar da al’uma gaba, da yunkurin raya al’ada ke samarwa. Daga bayanan da ke fitowa daga waccan ma’aikata mai jibi da tarihi da al’adu ta Kano, “History and Culture Bureau”, sun fadi cewa, wannan biki da a turance aka kira shi da “First Kano Festibal of Arts and Culture (KANFEST, 2025), an shirya shi ne bisa wasu manyan makasudai da kuma wasu manufofi da ake son cimmawa. Da farko, wannan hukuma, ta ayyana cewa, ta shirya wannan babban biki ne, don nuna kyawawan al’adu hada da fasahohin da Bahaushen Kano ke da shi, ko a ce ya gada kaka da kakanni. Kuma za a nunawa daukacin al’umar Duniya wannan biki, babu ragin-daka.

Bugu da kari, akwai wasu wasannin nishadi iri daban-daban masu kayatarwa da za a nuna su ga mahalarta taron, da ma waninsu. Wasannin Bahaushe, irin su wasannin Wanzamai, wasan wuta na Makera, wasan shan kankana na Manoma. Sannan, akwai baje-kolin basira daga gwanayen mabanbantan masu sana’o’in Malam Bahaushe, wadanda suma za su zalakarsu a ranakun bikin a Kano. Sana’o’in Majema, Masaka, Marina, Dukawa, da ma tsagin wasanni masu kayatarwa, suma za a nuna su ga mahalarta taron. Wasan “Yan-baka, wasan langa, wasan bago, “yar-carafke, gada, lugude, tafa-tafa, “yar gala-gala, kokawa, dambe, Malam na bakin kogi…da sauransu, duka za a nuna su daya bayan daya.

Tamkar irin yadda aka fara shirya wannan taro a matakin kasa bakidaya a Shekarar 1977, ita ma wannan hukuma da ta shirya taron a Kano, na da kudirin ci gaba da shirya bikin a duk Shekara, tamkar irin yadda manyan kasashen Duniya da suka ci gaba a yau suke shiryawa. Ba ya ga wasannin kwaikwayo na nishadi da ilmantarwa da za a nuna a ranakun bikin, suma kananan yara ba a bar su a baya ba, suma za su zo, tare da baje-kolin irin baiwar da Allah Yai musu. Jama’ar kowace karamar hukuma a Kano, za su halarci wannan biki da ake kokarin gudanarwa. Sannan, kowane 6angare na kananan hukumomin, za su zo tare da nuna irin baiwa, hazaka da fasahohin da suka yi shuhura akai, a ranakun bikin.

Kano
Muktar Anwar
+ postsBio
  • Muktar Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/muktar-anwar/
    Budaddiyar Wasika Ga Gwamnan Kano Abba K. Yusuf
  • Muktar Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/muktar-anwar/
    Yaduwar Juyin Mulki A Afirka
  • Muktar Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/muktar-anwar/
    Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
  • Muktar Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/muktar-anwar/
    Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

MASU ALAKA

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki
Bakon Marubuci

Yayin Da Dangote Ya Bayyana A Ganawar Neman Aiki

June 12, 2026
A Karshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Damar Yin Takara
Bakon Marubuci

A Karshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Damar Yin Takara

June 12, 2026
‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa
Bakon Marubuci

‘Symbolic Interactionism’:Sabuwar Makaranta A Kimiyyar Zamantakewa

June 5, 2026
Next Post
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

‘Yan Nijeriya Na Karbar Sakamakonsu Da Hannun Hagu A Wajen Tinubu - Atiku

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.