• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Kawo Karshen Barnata Karafunan Hanyar Jiragen Kasa A Nijeriya

by Leadership Hausa
2 years ago
in Manyan Labarai
0
A Kawo Karshen Barnata Karafunan Hanyar Jiragen Kasa A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ko ina a fadin Duniya, harkar saye da sayar da karafuna (‘Yan Kyadi ko ‘yan gwangwani) harka ce mai kawo alhairai masu yawa. A wani kiyasin da aka yi, bayani ya nuna ana samun fiye da Dala Biliyan 70 a harkar saye da sayar da karafuna a duniya a duk shekara.

A bayanin da kungiyar masu safarar karafuna da masu tattara da bola ta kasa (NASWDEN) suka yi, harkar masu Gyadi na tallafa wa harkokin sana’o’in al’umma a Nijeriya na fiye da Naira Tiriliya 1 a duk shekara.

  • Yadda Tinubu Ya Yi Nasara Kan Abokan Hamayyarsa Atiku Da Obi
  • Gwarzon ÆŠan Ƙwallon Duniya Ta Ballon D’or: Yaushe Za A Bayar Kuma Wa Zai Lashe?

An kafa kungiyar NASWDEN mai akalla mambobi fiye da mutum 35,000 a johihi 36 na kasar nan, an kafa ta ne a shekarar 2005 da nufin daidaita ayyukan dillalai da dukkan masu hada-hada a bangaren tattaro karafa da abubuwa a bola wadanda ake sake sarrafa su don fitar da wasu abubuwan amfani ga al’umma. Duk da harkokin kasuwanci yana tafiya daidai ga masu wannan sana’ar, sai dai a halin yanzu sana’ar na fuskantar wata babbar barazana saboda wasu bata gari sun shiga cikin harkokin sana’ar inda suke neman bata sana’ar ta hanyar saye da sayar da kayayyakin sata.

A cikin wata uku da suke wuce an samu rahottanni fiye da dozin na yadda jami’an tsaro suke kama manyan motoci shake da karafunan hanyar jirgin kasa a kusan dukkan sassan kasar nan. Wannan zai sanya mutum ya yanke hukuncin cewa, lallai akwai wasu da ke Shirin durkusar da zirga-zirgar jirgin kasa ta hanyar satar karafunan hanyar jiragen kasar ana sayar da su da sunan gyadi. Abin ya zama a duk mako sai wata rundunar tsaro ta bayar da rahoton kama mota shake da karafunan hanyar jirgi ko wasu karafunan da jirgin kasa ke amfani da shi.

Rahoton na wadanda aka kama ne a kan hanyarsu amma daga dukkan alamu ba za a rasa wasu manyan motocin dauke da irin wadanna kayan da suka samu nasarar tsallakewa ba. Satar kayayyakin hukumar jiragen kasa wani abu ne da aka yi shekaru ana tafkawa amma bambancin a halin yanzu shi ne yadda lamarin yake faruwa ba kakkautawa, hakan kuma na bayar da matukar tsoro.

Labarai Masu Nasaba

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

A kwanan nan ne, ranar 29 ga watan Agusta 2023, jami’an sojoji da ke aiki a karkashin shirin nan na ‘Operation Safe Haben’ da kuma ‘Hakorin Damisa IB’ suka bayar da rahoton kama wata babbar mota shake da karafunan jiragen kasa, an kama su ne a kan hanyar kauyen Gidan Ado da ke karamar hukumar Riyom ta Jihar Filato. Kwanaki 12 kafin wannan kamun kuma hukumar tsaron farin kaya ta (NSCDC) ta sanar da kama babbar mota kirar DAF dauke da karafunan hanyar jirgi an lullube su da wasu karafunan daban. A ranar 14 ga watan Agusta aka yi wannan kamun, an samu nasarar cafke mutum 4 da suka yi shigar Baban Bola. Haka kuma bayani ya nuna cewa, hukumar NSCDC ta samu nasarar cafke mutum 12 da ake zargi da laifin barnatar da karafunan hanyar jirgi, da ke a kan hanyar Kafanchan zuwa Kwai a Jihar Kaduna, da hanyar jirgin da aka shinfida a tsakanin Agwan zuwa kauyen Kuje a yankin Abuja da kuma na Nasarawa zuwa sansanin ‘yan yi wa kasa hidima (NYSC) da ke a kan hanyar Keffi zuwa Abuja. Haka kuma a ranar 7 ga watan Yuli rundunar ‘yansanda na Jihar inugu ta bayar da rahoton kama mutum biyu da ake zargi da barnatar da kayayyakin hukumar jiragen kasa, an kama barayin ne a garin Emene da ke kan babbar hanyar Inugu zuwa Abakaliki. A ranar 5 ga watan Yuli 2023 rundunar hukumar NSCDC ta samu nasarar kama manyan motoci 2 dauke da karafunan hanyar jirgi a garin Olooru da ke Jihar Kwara an samu nasarar kama mutum 6 da ake zargi a kan hanyarsu ta dawowa daga kauyen Jagundi ta karamar hukumar Kafanchan ta Jihar Kaduna.

Haka kuma a ranar 15 ga watan Yuni a garin Doma ta Jihar Nasarawa Sojoji sun samu nasarar kama mutum 12 da ake zargi da lallata tare da sace karafunan hanyar jirin kasa a Angwan Yara da Agyaragu a karamar hukumar Keana ta Jihar Nasarawa. Jami’n hulda da jama’a na runduna ta musamman ta 4 da ke Doma ya bayyana cewa, wadanda ake zargin sun yi ta kokarin ba sojojin cin hanci, inda har suka bayar da Naira Miliyan 5 don su kauce wa kamun sojojin.

Akwai rahotanni da dama na yadda barayin karafunan jirgi ke kokarin ba jami’an tsaro cin hanci don a bar su su wuce a kan hanyoyinmu. A ra’ayinmu bai isa kawai rahotannin kamun barayin karafunan hanyar jirgin kasa da ake yi ba, ya kamata jami’an staro su kara zurfafa bincikensu don gano masu kitsa harkar sace-sacen da ake yi da kuma wadanda suke a kan gaba wajen sayen karafunan. Ba za a iya samun nasara a wajen wannan kokarin ba sai an samu hadin kan kungiyar dillalai da masu saye da sayar da kyadi na kasa da kuma kungiyar masu motoci na kasa. In har wannan lamarin ya ci gaba a haka, nan gaba kadan ba za a samu karafuna hanyar jiragen kasar ba a sassan kasar nan wanda hakan zai mautukar shafar ci gaba da bunkasar tattalin arzikin kasa. Saboda haka dole a dauki matakin kawo karshen wannan mummunan aikin.

Akwai masu harkar saye da sayar da karafuna na gaskiya a sassan Nijeriya musamman a jihohin Ogun, Legas, Filato da Ribas. Saboda haka akwai bukatar su fito su kare sana’arsu kafin a ci gaba da danganta sana’ar Kyadi da sata. Nijeriya ta ci bashin makudan kudade don inganta harkokin zirga-zirgan jirgin kasa a ‘yan shekarun nan. Hanyar jirgi daga Abuja zuwa Kaduna mai stawon kilomita 187 ya lakume kusan Dala Biliyan 1, na Legas zuwa Ibadan mai tsawon kilomita 312 ya lakume Dala Biliyan 1.2 yayin da aka kashe Dala Biliyan 1.1 don samar da hanyar jirgin daga Kano zuwa Kaduna. Ana kuma bukatar fiye da Dala Biliyan 4 don hada hanyar jirgi daga Legas zuwa Kalaba wanda zai biyo ta Warri da Fatakwal. Ba zai yiwu gwamnati ta ci gaba da ciwo bashi don samar da ababen more rayuwa ba amma ana ci gaba da barnata su.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Gombe Ya Yaba Da Hukuncin Kotu Kan Tabbatar Da Nasarar Shugaba Tinubu

Next Post

Kurakuran Da Ke Ingiza Juyin Mulki A Afirka

Related

Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

56 minutes ago
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno
Manyan Labarai

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

4 hours ago
Sanusi
Manyan Labarai

‘Yansanda A Kano Sun GargaÉ—i Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

15 hours ago
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

19 hours ago
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus
Manyan Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

21 hours ago
Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

1 day ago
Next Post
Kurakuran Da Ke Ingiza Juyin Mulki A Afirka

Kurakuran Da Ke Ingiza Juyin Mulki A Afirka

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 4, 2025
katsina

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

June 4, 2025
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

June 4, 2025
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

June 3, 2025
Sanusi

‘Yansanda A Kano Sun GargaÉ—i Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

June 3, 2025
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

June 3, 2025
An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.