• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Kawo Karshen Mace-mace A Hanyoyinmu

by Leadership Hausa and Sulaiman
8 months ago
in Labarai
0
Mutum 3 Sun Rasu, 15 Sun Jikkata A Wani Hadarin Mota A Hanyar Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hanyoyin Nijeriya sun zama hanyoyi dake da ban tsoro masu sanadiyar rasa rayukan jama’a. Daga cikinsu akwai na kwana kwanan nan, hatsarin da a ka yi a Kaduna inda mutum arba’in suka rasu a kan hanyar su ta zuwa wurin bilin maulidi.

 

Motar da suke ciki ne ta yi taho mu gamu da wata tankar mai a hanyar Saminaka kta kramar hukumar Lere, a Jihar Kaduna.

  • Kaso 40 Na ‘Yan Nijeriya Na Samun Wutar Lantarki Fiye Da Awa 20 A Kowace Rana — Minista
  • Kirkirar Kimiyya Da Fasaha Ta Kasar Sin Na Sa Kaimi Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

Kwanaki kadan kafin wannan, wani mummunan hatsarin da ya afku a Jihar Neja inda ya yi sanadiyyar rasuwar mutum arba’in da takwas bayan wata takar mai ta hade da tifa wanda ya yi sanadiyyar mummunar fashewa.

Wata daya kafin wannan nan kuma, an samu hatsari  daban-daban a Jihar Oyo da Ogun inda mutum talatin da bakwai da ashirin da biyar suka rasu a ranadaya a babbar hanyar Ibadan zuwa Legas.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Wannan ba kawai kididdiga ba ne, wannan yana nuna  yadda mutane ke rasa rayukansu ta hanyar da za a iya kiyayewa.

Duk da yadda yawan adadin mutanen da suke rasuwa ta hanyar hatsari ya ragu a shekara 2023, da kimanin mutum 5,081 idan a ka kwatanta da mutum 6,456 da suka rasu a shekarar 2022, kamar yadda hukumar kula da hanyoyi a Nijeriya ta bayyana.

Nijeriya tana cikin kasashe masu yawan mutuwa a kan tituna a duk duniya da kaso 33.7 a cikin mutum 100,000 wanda ya wuce yadda ya kamata wato kaso 17.4.

Mu dawo dashi daidai, kason da ya kamata ya tsaya a duniya shi ne, 17.4 duk mutum 100,00. Inda kasar Zimbabwe take kan gaba da kimanin mutuwar mutane 74.5 duk daga cikin mutum 100,000.

Dililan da suke janyo wannan mace-macen a kan hanyoyi sannannu ne kuma kididdigaggu. Gudun wuce  kima  shima yana kan gaba inda direbobi suke wuce iyakan da aka sanya domin samun riba mai yawa musamman a motocin haya.

Tukin ganganci, gajiya, da kuma oba lod a motoci da kuma tuki cikin dare ne suke kara girmama hatsarin.

A ‘yan shekarun nan, yawan anfani da wayar hannu a lokacin tuki ya kara munana lamarin. Inda direbobin da hankalinsu ya dauke suke jawo hatsari. Ko ta hanyar daukar waya, tura sakonni, ko kuma duba shafukan sada zumunta, wadannan abubuwan da ke dauke hankali sun nuna suna da hatsari sosai.

Lalacewar hanyoyin Nijeriya kuma yana kara hauhwar matsalar. Manyan tituna sun lalace da ramuka, kuma ba tare da alamun hanya masu kyau ba inda hatta direbobi masu kiyayewa ke iya fadawa cikin hatsari.

Duk da ana yawan zargin direbobi masu zaman kansu, lalacewa da kuma rashin gyara da kuma kawo karshen lalatattun hanyoyi na cikin abubuwa masu tada hankali.

Abun takaicin shi ne masu kula da dokokin hanya sun mayar da hankalinsu wajen kananan abubuwan da basu da muhimmanci kamar takardun mota, inda suka mai da hakan hanyar samun kudi maimakon wajen kare rayukan mutane.

Tsofaffin hanyoyin magance hadurran da muke amfani dasu sun gaza. A wasu kasashen duniya kimiyya ya taka rawar gani wajen magance mace mace a hanyoyi ta hanyar anfani da kamarorin duba gudu da kuma na’urorin agajin gaggawa. A Nijeriya, wannan ci gaban ya yi karanci, hakan  abin yake barin hanyoyin a lalace fiye da yadda ya kamata su zama.

Ilimin direbobi shi ma babban abin lura ne. Hanyar samun lasisi a Nijeriya cike yake da cin hanci, hakan yake barin direbobin da basu cacanta ba suna samun lasisi ba tare da horon da ya dace ba. Ya kamata a sauya tsarin samun lasisin, a kuma maida hankali wajen ilmantarwa, gwaji da kuma horar da direbobin.

Mace-macen rayuka a kan hanyoyi na tada hankali. Hatsari a hanyoyi ya zama hanya na biyu da yake kawo mace mace wanda ya wuce ayyukan Boko Haram da ‘yan ta’adda. Duk da ana maida hankali wajen su wadancan kalubalen, mace-macen da a ke samu a hanyoyi su ma suna  tayar da hankali.

Hadarurruka na da tasiri a fannin tattalin arziki. Asibitoci, sun riga sun cika kuma babu isasshen kayan aiki ga majinyantan hatsarruka a kwance. Iyalai na fuskantar barazana ta hanyar rasa jigogin iyalin, kasuwanci na samun tsaiko wajen samun kayayyaki da kuma tafiyar ma’aikata.

Wadannan su ne hanyoyin da ta kamata gwamnati ta dauka, na farko,  zuba jari da kuma manyan ayyuka a hanyoyi. Manyan hanyoyi na bukatar gyara a kai a kai, dole a gyara ramuka, a samar da wuta,da kuma alamun nuni a hanyoyi. Wadannan ci gaban za su iya samar da gagarumin sauyi wajen kare afkuwar hadurra.

Kimiyya da fasaha na taka rawar gani wajen kiyaye hadurra. A samar da kamarori, musamman a wajen da suke da hadari, wannan zai rage guje guje da kuma tukin ganganci. A kuma samar da wajen samar da agajin gaggawa a kusa da manyan hanyoyi su zama a shirye wajen kawo dauki idan an samu hadurra.

Tsaurara dokin tuki a hanyoyi shima wani babban hanya ce. Hukumar Kare Hadurra da sauran masu sa ido dole a samar masu da kayan aiki kuma a sa masu ido domin tabbatar da suna aiki yadda ya kamata. Wannan ya hada da kama masu gudun ganganci, masu shaye shaye yayin tuki, da kuma masu yin wasu abubuwa yayin da suke tukin. A samar da tara ga duk wanda ya karya dokokin ya zama mai tsanani saboda ta zama izinina ga saura. Sannan kuma a dauki mummunan mataki a kan masu nanata laifi.

Ilimin direbobi na da matukar muhimmanci, wannan hanyar samun lasisin dole a canza shi da tsari mai kyau wanda kuma za a tabbatar da bin doka a ciki. Ya zama direbobi na fuskantar tantancewa, da kuma horo wa da zai sanya masu al’adun tuki a tattare dasu. A kuma tsananta wayar da kan jama’a masu amfani da hanyoyi  akan hadurra da kuma yadda ganganci ke jawo aukuwarsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamna Radda Ya Tallafa Wa Mata 8,000 Da Naira Miliyan 4 A Katsina 

Next Post

Wakilin Sin: Ya Kamata A Kiyaye Da Karfafa Gudummawar MDD A Fannin Yaki Da Ta’addanci

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

8 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

9 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

10 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

14 hours ago
mace-mace
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

15 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

16 hours ago
Next Post
Wakilin Sin: Ya Kamata A Kiyaye Da Karfafa Gudummawar MDD A Fannin Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin: Ya Kamata A Kiyaye Da Karfafa Gudummawar MDD A Fannin Yaki Da Ta’addanci

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.