• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Mai Da Duniya Ta Zama Ta Kasa Da Kasa

by CGTN Hausa and Sulaiman
7 months ago
Duniya

A wannan mako, gwamnatin kasar Amurka ta sanar da dakatar da gudummawar da take samarwa Ukraine ta fannonin soja da ma leken asiri, biyowa bayan fadan da shugabannin kasashen biyu suka yi a ranar 28 ga watan da ya gabata a fadar White House, inda da ma suka yi shirin daddale yarjejeniyar ma’adinai. Sakamakon fadan, shugaban Ukraine ya bar White House ba tare da rattaba hannu a kan yarjejeniyar ba, don haka Amurka ta dakatar da gudummawar soja da ta leken asiri da take ba kasar Ukraine. 

Lallai tsawon shekaru uku bayan aukuwar yaki a tsakanin Ukraine da Rasha, sabuwar gwamnatin Amurka ta zamanto “mai son wanzar da zaman lafiya” a tsakanin kasashen biyu daga wadda ta yi ta rura wutar rikicin tun farko. Har ma ta fake da sunan “Wanzar da dadadden zaman lafiya”, don bukatar Ukraine ta daddale yarjejeniyar ma’adinai da ita. Bisa ga yarjejeniyar, sassan biyu za su kafa wani asusu, wanda Amurka ke bukatar Ukraine ta zuba rabin kudaden da ta samu daga albarkatun ma’adinai na kasar cikinsa, har ma take yunkurin sa hannunta cikin ababen samar da mai da iskar gas na kasar. Akwai wani sharhin wata kafar yada labarai dake cewa, a zahiri hakan ya kasance yarjejeniyar mulkin mallaka ta fannin tattalin arziki a cikin karni na 21. Ai ba sabo da zaman lafiya sabuwar gwamnatin Amurka ke neman kawo karshen matsalar Ukraine ba, a’a, abin da take so shi ne ta ci karin moriya ta fannin tattalin arziki, kuma ta saba da yin hakan don cimma manufarta ta wai “Ba Amurka fifiko”.

  • Za Mu Bai Wa Maraɗa Kunya A Wasanmu Da Manchester United – Arteta
  • Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku

Mujallar The Economist ta wallafa wata mukala a shafinta a kwanakin baya cewa, shugaba Donald Trump ya fara neman iko a kasashen duniya ta hanyar nuna fin karfi da danniya, wanda hakan ya bayyana a fili a kasar Ukraine. Mukalar ta kuma yi nuni da cewa, yadda nuna fin karfi ya kasance tamkar “mai adalci” kuma ake cin zalin kasashe marasa karfi, na kara tabbata a duniyarmu.

Amma da gaske ne hakan zai tabbata? Ban yarda ba.

A gun taron wanzar da zaman lafiya da aka kira a birnin Paris sama da shekaru dari da suka wuce, Sinawa sun taba tambayar ko, “adalci ne zai ci galaba a kan fin karfi”, ko kuma “nuna fin karfi ne zai ci nasara a kan adalci?” A game da wannan, ministan wajen kasar Sin Wang Yi ya ba da taikamaimiyar amsa a taron manema labarai da aka kira game da harkokin diplomasiyya a kwanakin baya, a gefen taron shekara shekara na majalisar wakilan jama’ar kasar da ke gudana a birnin Beijing, inda ya ce, bai kamata a mayar da hannun agogo baya ba. Kamata ya yi manyan kasashe su dauki nauyin da duniya ta dora a wuyansu, a maimakon su mai da hankali kawai a kan moriyarsu ko kuma su yi wa kasashe marasa karfi danniya.

LABARAI MASU NASABA

Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa

Abin haka yake, akwai kasashe sama da 190 a duniyarmu, idan kowace kasa na bin manufar ba kanta fifiko, to nuna fin karfi zai zama a ko ina a duniyarmu, kuma kasashe masu karamin karfi su ne za su fi fuskantar matsalar. Amma abin farin ciki shi ne, har yanzu akasarin kasashen duniyarmu na rungumar adalci da zaman daidaito, kuma karin kasashe na rungumar gina al’umma mai kyakkyawar makoma ga dukkan bil’adama. A sa’i daya kuma, kasashe masu tasowa na kara karfinsu, inda suka riga suka zama muhimmin karfin da ke kiyaye zaman lafiya da sa kaimin ci gaban duniya.

Mutanen kasashen yamma su kan ce, “Moriya ta fi zumunta muhimmanci da dorewa”. Amma a ganin Sinawa, ya kamata abota ta dore har abada, kuma hakan zai tabbatar da moriyar kowa. Kamar dai yadda ministan wajen kasar Sin Wang Yi ya fada, “Tarihi zai shaida cewa, wadanda suke rungumar kowa, su ne za su ci nasara. Hada kan juna don gina al’umma mai kyakkyawar makoma ga dukkan bil’adama, zai mai da duniyarmu ta zama ta kasa da kasa, tare da tabbatar da kyakkyawar makoma ta bai daya ga kowa.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang
Ra'ayi Riga

Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang

October 13, 2025
Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa
Ra'ayi Riga

Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa

October 12, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka
Ra'ayi Riga

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Next Post
Nazarin CGTN: Mutane Da Dama A Duniya Sun Yaba Da Salon Shugabancin Gwamnatin Kasar Sin 

Nazarin CGTN: Mutane Da Dama A Duniya Sun Yaba Da Salon Shugabancin Gwamnatin Kasar Sin 

LABARAI MASU NASABA

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025
Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

October 19, 2025
Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.