ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

A Mai Da Duniya Ta Zama Ta Kasa Da Kasa

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Duniya

A wannan mako, gwamnatin kasar Amurka ta sanar da dakatar da gudummawar da take samarwa Ukraine ta fannonin soja da ma leken asiri, biyowa bayan fadan da shugabannin kasashen biyu suka yi a ranar 28 ga watan da ya gabata a fadar White House, inda da ma suka yi shirin daddale yarjejeniyar ma’adinai. Sakamakon fadan, shugaban Ukraine ya bar White House ba tare da rattaba hannu a kan yarjejeniyar ba, don haka Amurka ta dakatar da gudummawar soja da ta leken asiri da take ba kasar Ukraine. 

Lallai tsawon shekaru uku bayan aukuwar yaki a tsakanin Ukraine da Rasha, sabuwar gwamnatin Amurka ta zamanto “mai son wanzar da zaman lafiya” a tsakanin kasashen biyu daga wadda ta yi ta rura wutar rikicin tun farko. Har ma ta fake da sunan “Wanzar da dadadden zaman lafiya”, don bukatar Ukraine ta daddale yarjejeniyar ma’adinai da ita. Bisa ga yarjejeniyar, sassan biyu za su kafa wani asusu, wanda Amurka ke bukatar Ukraine ta zuba rabin kudaden da ta samu daga albarkatun ma’adinai na kasar cikinsa, har ma take yunkurin sa hannunta cikin ababen samar da mai da iskar gas na kasar. Akwai wani sharhin wata kafar yada labarai dake cewa, a zahiri hakan ya kasance yarjejeniyar mulkin mallaka ta fannin tattalin arziki a cikin karni na 21. Ai ba sabo da zaman lafiya sabuwar gwamnatin Amurka ke neman kawo karshen matsalar Ukraine ba, a’a, abin da take so shi ne ta ci karin moriya ta fannin tattalin arziki, kuma ta saba da yin hakan don cimma manufarta ta wai “Ba Amurka fifiko”.

  • Za Mu Bai Wa Maraɗa Kunya A Wasanmu Da Manchester United – Arteta
  • Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku

Mujallar The Economist ta wallafa wata mukala a shafinta a kwanakin baya cewa, shugaba Donald Trump ya fara neman iko a kasashen duniya ta hanyar nuna fin karfi da danniya, wanda hakan ya bayyana a fili a kasar Ukraine. Mukalar ta kuma yi nuni da cewa, yadda nuna fin karfi ya kasance tamkar “mai adalci” kuma ake cin zalin kasashe marasa karfi, na kara tabbata a duniyarmu.

ADVERTISEMENT

Amma da gaske ne hakan zai tabbata? Ban yarda ba.

A gun taron wanzar da zaman lafiya da aka kira a birnin Paris sama da shekaru dari da suka wuce, Sinawa sun taba tambayar ko, “adalci ne zai ci galaba a kan fin karfi”, ko kuma “nuna fin karfi ne zai ci nasara a kan adalci?” A game da wannan, ministan wajen kasar Sin Wang Yi ya ba da taikamaimiyar amsa a taron manema labarai da aka kira game da harkokin diplomasiyya a kwanakin baya, a gefen taron shekara shekara na majalisar wakilan jama’ar kasar da ke gudana a birnin Beijing, inda ya ce, bai kamata a mayar da hannun agogo baya ba. Kamata ya yi manyan kasashe su dauki nauyin da duniya ta dora a wuyansu, a maimakon su mai da hankali kawai a kan moriyarsu ko kuma su yi wa kasashe marasa karfi danniya.

LABARAI MASU NASABA

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

Abin haka yake, akwai kasashe sama da 190 a duniyarmu, idan kowace kasa na bin manufar ba kanta fifiko, to nuna fin karfi zai zama a ko ina a duniyarmu, kuma kasashe masu karamin karfi su ne za su fi fuskantar matsalar. Amma abin farin ciki shi ne, har yanzu akasarin kasashen duniyarmu na rungumar adalci da zaman daidaito, kuma karin kasashe na rungumar gina al’umma mai kyakkyawar makoma ga dukkan bil’adama. A sa’i daya kuma, kasashe masu tasowa na kara karfinsu, inda suka riga suka zama muhimmin karfin da ke kiyaye zaman lafiya da sa kaimin ci gaban duniya.

Mutanen kasashen yamma su kan ce, “Moriya ta fi zumunta muhimmanci da dorewa”. Amma a ganin Sinawa, ya kamata abota ta dore har abada, kuma hakan zai tabbatar da moriyar kowa. Kamar dai yadda ministan wajen kasar Sin Wang Yi ya fada, “Tarihi zai shaida cewa, wadanda suke rungumar kowa, su ne za su ci nasara. Hada kan juna don gina al’umma mai kyakkyawar makoma ga dukkan bil’adama, zai mai da duniyarmu ta zama ta kasa da kasa, tare da tabbatar da kyakkyawar makoma ta bai daya ga kowa.”

Duniya
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Xi Da Kim Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Yarjejeniyar Abota, Hadin Gwiwa Da Taimakon Juna Tsakanin Sin Da DPRK
Duniya
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce
  • Sulaiman
    Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya
  • Sulaiman
    Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani
  • Sulaiman
    Xi Da Kim Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Yarjejeniyar Abota, Hadin Gwiwa Da Taimakon Juna Tsakanin Sin Da DPRK

MASU ALAKA

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka
Ra'ayi Riga

“Kashin Baya” Na Sin Ya Zama Abun Dogara Ga Kasashen Afirka

July 10, 2026
Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Aka Ce Kasar Sin Ta Ceci Tattalin Arzikin Duniya?

July 9, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Next Post
Nazarin CGTN: Mutane Da Dama A Duniya Sun Yaba Da Salon Shugabancin Gwamnatin Kasar Sin 

Nazarin CGTN: Mutane Da Dama A Duniya Sun Yaba Da Salon Shugabancin Gwamnatin Kasar Sin 

LABARAI MASU NASABA

Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

July 11, 2026
Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

July 11, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
Xi Da Kim Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Yarjejeniyar Abota, Hadin Gwiwa Da Taimakon Juna Tsakanin Sin Da DPRK

Xi Da Kim Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Yarjejeniyar Abota, Hadin Gwiwa Da Taimakon Juna Tsakanin Sin Da DPRK

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina

July 11, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
NAF Ta Kai Hare-Haren Sama Kan Maboyar Ƴan Ta’adda A Borno

NAF Ta Kai Hare-Haren Sama Kan Maboyar Ƴan Ta’adda A Borno

July 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.