Tsohon Shugaban Ƙasa, Olusegun Obasanjo, ya bayyana cewa marigayi Janar Sani Abacha, ya tsara kashe shi, da Chief Moshood Abiola, da Janar Shehu Musa Yar’Adua yayin da suke tsare, domin tabbatar da cewa zai ci gaba da mulki har abada.
Obasanjo ya bayyana hakan ne yayin wata ziyarar da ya kai Ogbor Uvuru a ƙaramar hukumar Aboh Mbaise, Jihar Imo, inda ya kaddamar da sabuwar coci mai suna “The Noah’s Ark” na Assemblies of God, wanda fitaccen ɗan kasuwa Obioma Success Akagburuonye ya gina.
- Wata Gidauniyar Kasar Sin Ta Mika Ma’ajiyar Ruwa Ga Al’ummar Wani Kauyen Habasha
- Jami’ar Maryam Abacha Ta Rufe Ɗakunan Kwanan Ɗalibai Saboda Aikata Rashin Ɗa’a A Kano
Yayin da yake tunawa da lokacin da ya kwashe a gidan yari a ƙarƙashin mulkin Abacha, Obasanjo ya ce a farko ya ɗauka an kama shi ne bisa kuskure, amma daga baya ya fahimci cewa shiri ne na kashe shi. Ya ce Abacha ya faɗa a fili cewa ba zai bari su fita da rai daga gidan yari ba – shi kaɗai ne ya tsira, “ba da ƙarfina ba, sai dai da ikon Allah.”
Ya ƙara da cewa ya rungumi addu’a sosai a lokacin da yake tsare, yana addu’ar neman tsira daga masu zaluntarsa, kamar yadda Littafi mai tsarki ya ruwaito. “Na mika wuya gaba ɗaya ga Allah,” in ji shi.
Obasanjo ya kuma tuna wani lokaci a shekarar 1959 lokacin da ya halarci wani kwas a Ghana, yana bayani kan yadda abubuwan da suka faru a rayuwarsa suka gina shi, tare da jaddada cewa rahamar Allah ce ta ke ci gaba da kula da rayuwarsa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp