• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Faru Tsakanin Ukraine Da Rasha Bayan Barkewar Yaki A Gaza

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Labarai
0
Abin Da Ya Faru Tsakanin Ukraine Da Rasha Bayan Barkewar Yaki A Gaza
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A farkon watan Nuwamba, Ukraine ta bayar da rahoton cewa, an yi ruwan bama-bamai kan kimanin wurare 120 a cikin kwana daya, hari mafi girma tun bayan kamawar wannan shekarar.

Amma duk da haka hankalin duniya ya ci gaba da kasancewa a kan Gaza da Isra’ila.
Yiwuwar samun raguwar daga kasashen duniya, shi ne fargaba mafi muni ga kasar Ukraine tun daga lokacin da Rasha ta kaddamar da mamaya a kanta.

  • Rashin Adalci Ne Karbe Kashi 40 Cikin 100 Na Kudaden Shigar Jami’oi (1)
  • Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi Yayin Kwarya-kwaryar Taron Shugabannin APEC

Idan babu tallafin soji da na kudi daga kawayenta, Ukraine ba za ta samu wata dama ba wajen tunkarar Rasha a fagen daga da kuma kiyaye farmaki ta sama, wanda ke da matukar muhimmanci ga kare garuruwan Ukraine.

Bari mu duba wasu daga cikin manyan abubuwan da suka faru a fagen daga tsakanin Rasha da Ukraine.
Yakin Juriya

Manazarta da dama sun ce bangaren da zai iya jure wa hasara na tsawon lokaci shi ne zai yi nasara a yakin.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Kwamandan dakarun Ukraine, Balery Zalumzhny ya bayyana yakin a matsayin “mai gajiyarwa.”

“Kamar yadda ya faru a yakin duniya, mun kai wani matsayi na ci gaban kere-kere da za a iya cewa an kai bango,” kamar yadda ya bayyana a wata mukala a jaridar ‘the Economist’ ta Birtaniya.

A wani bayani kan wata biyar da sojojin Ukraine suka kwashe suna kokarin kwato yankunan da Rasha ta kwace, ya ce a tsawon wata biyar, sojojin sun matsa a yankin da bai wuce kilomita 17 ba.

A halin yanzu Rasha na iko da kimanin kashi 17.5% na fadin kasa mallakin Ukraine, duk da an samu sauyi a 2023.

A makonnin da suka gabata fada ya kazanta a kusa da garin Abdiibka da ke gabashin Ukraine, inda dukkanin bangarorin biyu suka yi asarar dakaru ba tare da wata nasarar a zo a gani ba.

Ma’aikatar tsaron Birtaniya ta yi kiyasin cewa asarar da Rasha ta yi a garin Abdiibka a shekarar 2023 ta fi ta kowane lokaci.

Janar Zalunzhny ya bayyana yadda a yanzu bangarorin biyu ke takama da kayan yaki na zamani, ta yadda kowa na iya ganin abin da abokin hamayyarsa ke kitsawa.

Ya ce sanadiyyar hakan ne dukkanin bangarorin biyu suka kasa samun nasarar a-zo a -gani.

Daga nan sai ya yi kira ga kawayen Ukraine da su samar wa kasar da makamai masu tsananin saiti, da kuma makaman atilare.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaRashaUkraine
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojojin Mali Sun Kwace Muhimmiyar Tungar ‘Yan Tawayen Kidal

Next Post

Dalilan Da Suka Sa Turawa Samun Nasarar Mulkin Mallaka A Arewa

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

4 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

5 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

6 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

10 hours ago
Ukraine
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

11 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

12 hours ago
Next Post
Dalilan Da Suka Sa Turawa Samun Nasarar Mulkin Mallaka A Arewa

Dalilan Da Suka Sa Turawa Samun Nasarar Mulkin Mallaka A Arewa

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.