• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Faru Tsakanin Ukraine Da Rasha Bayan Barkewar Yaki A Gaza

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Ukraine

A farkon watan Nuwamba, Ukraine ta bayar da rahoton cewa, an yi ruwan bama-bamai kan kimanin wurare 120 a cikin kwana daya, hari mafi girma tun bayan kamawar wannan shekarar.

Amma duk da haka hankalin duniya ya ci gaba da kasancewa a kan Gaza da Isra’ila.
Yiwuwar samun raguwar daga kasashen duniya, shi ne fargaba mafi muni ga kasar Ukraine tun daga lokacin da Rasha ta kaddamar da mamaya a kanta.

  • Rashin Adalci Ne Karbe Kashi 40 Cikin 100 Na Kudaden Shigar Jami’oi (1)
  • Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi Yayin Kwarya-kwaryar Taron Shugabannin APEC

Idan babu tallafin soji da na kudi daga kawayenta, Ukraine ba za ta samu wata dama ba wajen tunkarar Rasha a fagen daga da kuma kiyaye farmaki ta sama, wanda ke da matukar muhimmanci ga kare garuruwan Ukraine.

Bari mu duba wasu daga cikin manyan abubuwan da suka faru a fagen daga tsakanin Rasha da Ukraine.
Yakin Juriya

Manazarta da dama sun ce bangaren da zai iya jure wa hasara na tsawon lokaci shi ne zai yi nasara a yakin.

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kwamandan dakarun Ukraine, Balery Zalumzhny ya bayyana yakin a matsayin “mai gajiyarwa.”

“Kamar yadda ya faru a yakin duniya, mun kai wani matsayi na ci gaban kere-kere da za a iya cewa an kai bango,” kamar yadda ya bayyana a wata mukala a jaridar ‘the Economist’ ta Birtaniya.

A wani bayani kan wata biyar da sojojin Ukraine suka kwashe suna kokarin kwato yankunan da Rasha ta kwace, ya ce a tsawon wata biyar, sojojin sun matsa a yankin da bai wuce kilomita 17 ba.

A halin yanzu Rasha na iko da kimanin kashi 17.5% na fadin kasa mallakin Ukraine, duk da an samu sauyi a 2023.

A makonnin da suka gabata fada ya kazanta a kusa da garin Abdiibka da ke gabashin Ukraine, inda dukkanin bangarorin biyu suka yi asarar dakaru ba tare da wata nasarar a zo a gani ba.

Ma’aikatar tsaron Birtaniya ta yi kiyasin cewa asarar da Rasha ta yi a garin Abdiibka a shekarar 2023 ta fi ta kowane lokaci.

Janar Zalunzhny ya bayyana yadda a yanzu bangarorin biyu ke takama da kayan yaki na zamani, ta yadda kowa na iya ganin abin da abokin hamayyarsa ke kitsawa.

Ya ce sanadiyyar hakan ne dukkanin bangarorin biyu suka kasa samun nasarar a-zo a -gani.

Daga nan sai ya yi kira ga kawayen Ukraine da su samar wa kasar da makamai masu tsananin saiti, da kuma makaman atilare.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure
Manyan Labarai

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 5, 2025
Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista
Labarai

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Labarai

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
Next Post
Dalilan Da Suka Sa Turawa Samun Nasarar Mulkin Mallaka A Arewa

Dalilan Da Suka Sa Turawa Samun Nasarar Mulkin Mallaka A Arewa

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 5, 2025
Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

November 5, 2025
Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

Majalisar Dattawa Ta Amince da Naira Tiriliyan 1.1 Don Biyan Bashin ‘Yan Kwangila – Akpabio

November 5, 2025
An Nemi Kasashen ECOWAS Su Samar Da Kariya Ga Yankunan Hakar Ma’adanai

ECOWAS Ta Ƙaryata Iƙirarin Trump Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

Tsohon Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ya Rasu Yana Da Shekaru 86

November 5, 2025
Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

Ɗan Majalisar Amurka Ya Zargi Kwankwaso Da Hannu A Kisan Kiristoci A Nijeriya

November 5, 2025
Sanata Barau Ya Tsaya Takarar Shugaban Majalisar Dattawa

Ba Na Jin Tsoron Trump – Martanin Sanata Barau Ga Akpabio

November 5, 2025
CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

CIIE Na Sin Karin Tagomashi Ne Ga Kasashen Afrika

November 5, 2025
Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.