• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Faru Tsakanin Ukraine Da Rasha Bayan Barkewar Yaki A Gaza

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Labarai
0
Abin Da Ya Faru Tsakanin Ukraine Da Rasha Bayan Barkewar Yaki A Gaza
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A farkon watan Nuwamba, Ukraine ta bayar da rahoton cewa, an yi ruwan bama-bamai kan kimanin wurare 120 a cikin kwana daya, hari mafi girma tun bayan kamawar wannan shekarar.

Amma duk da haka hankalin duniya ya ci gaba da kasancewa a kan Gaza da Isra’ila.
Yiwuwar samun raguwar daga kasashen duniya, shi ne fargaba mafi muni ga kasar Ukraine tun daga lokacin da Rasha ta kaddamar da mamaya a kanta.

  • Rashin Adalci Ne Karbe Kashi 40 Cikin 100 Na Kudaden Shigar Jami’oi (1)
  • Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi Yayin Kwarya-kwaryar Taron Shugabannin APEC

Idan babu tallafin soji da na kudi daga kawayenta, Ukraine ba za ta samu wata dama ba wajen tunkarar Rasha a fagen daga da kuma kiyaye farmaki ta sama, wanda ke da matukar muhimmanci ga kare garuruwan Ukraine.

Bari mu duba wasu daga cikin manyan abubuwan da suka faru a fagen daga tsakanin Rasha da Ukraine.
Yakin Juriya

Manazarta da dama sun ce bangaren da zai iya jure wa hasara na tsawon lokaci shi ne zai yi nasara a yakin.

Labarai Masu Nasaba

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

Kwamandan dakarun Ukraine, Balery Zalumzhny ya bayyana yakin a matsayin “mai gajiyarwa.”

“Kamar yadda ya faru a yakin duniya, mun kai wani matsayi na ci gaban kere-kere da za a iya cewa an kai bango,” kamar yadda ya bayyana a wata mukala a jaridar ‘the Economist’ ta Birtaniya.

A wani bayani kan wata biyar da sojojin Ukraine suka kwashe suna kokarin kwato yankunan da Rasha ta kwace, ya ce a tsawon wata biyar, sojojin sun matsa a yankin da bai wuce kilomita 17 ba.

A halin yanzu Rasha na iko da kimanin kashi 17.5% na fadin kasa mallakin Ukraine, duk da an samu sauyi a 2023.

A makonnin da suka gabata fada ya kazanta a kusa da garin Abdiibka da ke gabashin Ukraine, inda dukkanin bangarorin biyu suka yi asarar dakaru ba tare da wata nasarar a zo a gani ba.

Ma’aikatar tsaron Birtaniya ta yi kiyasin cewa asarar da Rasha ta yi a garin Abdiibka a shekarar 2023 ta fi ta kowane lokaci.

Janar Zalunzhny ya bayyana yadda a yanzu bangarorin biyu ke takama da kayan yaki na zamani, ta yadda kowa na iya ganin abin da abokin hamayyarsa ke kitsawa.

Ya ce sanadiyyar hakan ne dukkanin bangarorin biyu suka kasa samun nasarar a-zo a -gani.

Daga nan sai ya yi kira ga kawayen Ukraine da su samar wa kasar da makamai masu tsananin saiti, da kuma makaman atilare.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaRashaUkraine
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojojin Mali Sun Kwace Muhimmiyar Tungar ‘Yan Tawayen Kidal

Next Post

Dalilan Da Suka Sa Turawa Samun Nasarar Mulkin Mallaka A Arewa

Related

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

1 hour ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

2 hours ago
UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

10 hours ago
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista
Labarai

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

11 hours ago
gaza
Labarai

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

12 hours ago
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa
Labarai

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

14 hours ago
Next Post
Dalilan Da Suka Sa Turawa Samun Nasarar Mulkin Mallaka A Arewa

Dalilan Da Suka Sa Turawa Samun Nasarar Mulkin Mallaka A Arewa

LABARAI MASU NASABA

Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.