ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Da Suka Sa Turawa Samun Nasarar Mulkin Mallaka A Arewa

by Idris Aliyu Daudawa
3 years ago
Mulkin mallaka

Mulkin mallaka wata hanya ce ta tafiyar da gwamnati inda Turawan Ingila suka yi amfani da Sarakunan gargajiya wajen tafiyar da harkokin mulkinsu a yammacin Afirka. Shugaban ko jagoran al’amarin mulkin mallaka a yammacin Afirka shi ne Lord Frederick Lugard a shekarar1906.Ya fara gwada tafiyar da tsarin mulkin ne a Arewacin Nijeriya lokacin da aka ga abin an samu nasara,sai aka fara amfani da shi a sauran sassan kasashen yammacin Afirka.

An amince da Sarakunan gargajiya
Sarakuna wadanda sune ke lura da al’amuran da suka shafi al’umma a Arewacin Nijeriya al’umma suka nada su,don haka aka amince da sub a tare da wata matsala ba.Sune suka jagoranci hukumomin da ake tafiyar da al’amuran da suka shafi al’umma da ake kiran su da suna Natibe Authority. Shi ya sa babu wata matsala idan Sarakuna suka bayar da umarnin daya zo daga wurin jami’an Turawa na yin wani abu,hakan ta kasance ne saboda al’umma sun saba da samun umarni na wani abu daga wurin Sarakunan.

Sarakunan gargajiya ba su wasa da ba da umarni
Lokacin da gwamna Lord Lugard ya aiwatar da mulkin mallaka na Turawan Ingila a Arewacin Nijeriya,tun kafin lokacin da akwai hanyar da ake tafiyar da sarautar gargajiya ta tafiyar da al’umma.Sarakunan ko Sultan tuni akwai wuraren da suke karkashinsu suna mulkarsu ba tare da matsala ba,mutane kuma sun saba da al’amarin. Shi yasa mulkin ba a samu wata matsalar tafiyar da shi ba wanda yake da alaka da siyasa.

ADVERTISEMENT

Al’amarin Haraji
Al’ummar Arewacin Nijeriya sun saba da al’amarin daya shafi Haraji saboda kuwa Talakawa sun saba da biyan Haraji nau’oi daban daban da suka hada da Jangali na dabbobi da wadanda mutane suke biya,shi yasa ba a samu wata matsala ba domin al’ummar Arewa sun saba da biyan su nau’oin harajin,domin an samu yin gyara ne lokacin da aka bullo da shi lokacin da aka fara tafiyar da mulkin mallaka a Arewacin Nijeriya.

Rashin Masu Ilmin Zamani A Arewa
A Arewacin Nijeriya bamasu ilimin zamani a lokacin kamar yadda ake da su a Kudancin Nijeriya,saboda a lokacin a Arewacin Nijeriya akwai lauyoyi wadanda suka samu horo a Ingila da kuma ‘yan jarida,alal misali a Arewacin Nijeriya ba irin wadancan mutanen wadanda Turawan mulkin mallaka za su samu matsalar tunkararsu,ba kamar a Kudancin Nijeriya ba.

LABARAI MASU NASABA

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

Kotunan shariar musulunci
Mulkin mallaka na turawan Ingila ya samu nasara ne a Arewacin Nijeriya saboda dam tuni ana da tsarin shari’a karamar hukumar gargajiya da ake kira Natibe Authority a lokacin.Sarakuna a Arewacin Nijeriya suna da kotu inda ake shari’ar wadanda suka aikata laifi idan kuma aka samu mutum da aikata laifi ana iya yanke ma shi hukunci, wannan tsarin ne Lord Lugard ya amince da shi da yi ma shi gyara.Misali kotunan musulunci ba za su zartar da hukunci kisa ba, ba tare da amincewar jami’an Turawan mulkin mallaka da suke zaune a Larduna daban- daban a Nijeriya.

Umarnin Jami’an Ingila
Kasancewar jami’an Turawan Ingila a Arewacin Nijeriya inda suke kulawa da Larduna ana kiransu da sunan Rasdan sune suke ba Sarakunan gargajiya shawarwari, wanda hakan ne ya basu dama ta samun nasara a tafiyar da mulkinsu a Arewacin Nijeriya.Kwamishinonin Larduna su suka rika ba Sarakunan gargajiya a Arewa shawarar da ta tabbatar da mulkin Turawan Ingila ya samu nasara a yammacin Afirka.daudawa

Mulkin mallaka
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Sarakunan Da Suka Yi Wa Turawan Mulkin Mallaka Turjiya A Nijeriya
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kano Ta Yi Zarra Wajen Kashe Kuɗi Don Raya Ilimi A Yammacin Afirka
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Yajin Aiki: Ƙungiyar Likitocin Nijeriya Ta Ba Gwamnati Wa’adin Mako Huɗu

MASU ALAKA

Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Tarihi

Tarihin Shugaban Makaranta Na Farko A Arewa Hedimasta (2)

May 30, 2026
Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya
Tarihi

Cin Amana Uku Da Suka Sauya Tarihi A Duniya

February 22, 2026
Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959
Tarihi

Tarihin Sarkin Zazzau Ja’afaru Dan Isiyaku 1936-1959. (2)

January 11, 2026
Next Post
Nathan Tella: Matashin Da Ke Fatan Buga Wa Nijeriya Wasa

Nathan Tella: Matashin Da Ke Fatan Buga Wa Nijeriya Wasa

LABARAI MASU NASABA

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.