• English
  • Business News
Sunday, September 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Nijar Da Mali Da Burkina Faso Suka Fice Daga Kotun Duniya Ta ICC

by Rabi'u Ali Indabawa
3 hours ago
in Labarai
0
Abin Da Ya Sa Nijar Da Mali Da Burkina Faso Suka Fice Daga Kotun Duniya Ta ICC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasashen yankin Afirka ta yamma uku, Jamhuriyar Nijar da Mali da kuma Burkina Faso sun sanar da ficewar su daga kotun hukunta manyan laifuka ta ICC.

Kasashen sun bayyana cewa matakin nasu zai fara aiki ne nan take.

  • Matatar Dangote Ta Dawo Sayar Da Man Fetur A KuÉ—in Naira
  • Me Ya Sa Kamfanonin Jamus Fiye Da 560 Suka Zabi Wani Gari A Kasar Sin Don Gudanar Da Harkokinsu?

A cikin wata sanarwar hadin gwiwa, shugabannin sun zargi kotun da zamewa “‘‘yar koren masu mulkin mallaka” wadda take “nuna son zuciya wajen yin hukunci.”

Sanarwar wadda shugabannin kasashen suka fitar ta kuma zargi Kotun Hukunta Manyan Laifukan ta duniya da hukunta mutane daga kasashe marasa karfi, kuma ta nuna cewa “ta gaza” wajen hukunta laufuka mafi muni da ake tafkawa a doron kasa.

Wannan dai daya ne daga cikin matakan da kasashen uku suka dauka a baya-bayan nan bayan ficewarsu daga kungiyar hadin kan yammacin Afirka ta Ecowas, da kuma kafa kungiyar kasashen Sahle, wato AES.

Labarai Masu Nasaba

Majalisa Ta Daƙile PENGASSAN Akan Shirin Daina Kai Wa Matatar Ɗangote Gas Da Ɗanyen Mai

Matatar Dangote Ta Dawo Sayar Da Man Fetur A KuÉ—in Naira

A shekarar 2003 ne aka kafa kotun ta ICC wadda aka dorawa alhakin hukunta laifukan da suka shafi kisan kare dangi da cin zarafin bil’Adama da laifukan yaki kuma tun lokacin da fara aiki kotun ta ICC ta saurari kararraki 33

Masu sukar kotun ciki har da shugaban kasar Ruwanda Paul Kagame sun zargi kotun da nuna son zuciya ko rashin adalci saboda ta fai maida hanakli kan kasashen Afrika. Sai dai magoya bayan kotun sun ce rashin tasirin fannin shariar kasashen Afrika ne ya sa mutane ko gwamnatoci ke neman adalci a kotun ta ICC

kasashen yannkin Sahel uku wadanda a halin yanzu ke fama da rashin tsaro sakamakon hare-haren mayaka masu ikirarnin jihadi sun yanke alaka da wasu kasashen yamma da suka hada Faransa inda suka kulla kawance da Rasha domin samun tallafin soji da kuma inganta cinikayya tsakaninsu.

Kasashen 33 daga cikin 54 mambobi ne a kotun ta ICC kuma ta ta fara bincike a wasu kasashen Afrika da suka gada jamhuriyat tsakiyar afrika da jamhuriyar dimokradiyar Kongo da Kenya da Libya da kuma Mali sauran sun hada da Sudan da Uganda da kuma Iboyry cost Yarjebiyar kafa Yarjejeniyar da ta kafa kotun ta bai wa mambobinta damar janyewa, sai dai matakin zai fara aiki ne bayan shekara guda daga lokacin sanarwar.

A shekarar 2017, Burundi ta zama kasa ta farko kuma daya tilo daga Afirka da ta yi nasarar ficewa daga kotun ta ICC.

 

Mece ce kotun hukunta manyan laifuka, kuma mene ne aikinta?

Babban aikin kotun hukunta manayan laifuka shi ne gurfanarwa da kuma hukunta mutanen da ake zargi da aikata kisan kiyashi, da laifukan yaki da kuma sauran laifuakan cin zarafin bil’adama.

Haka nan kotun takan iya yin bincike tare da gurfanar da mutanen da ake zargi da aikata munanan laifuka da suka zamo abin damuwa tsakanin kasashen duniya.

Kotun takan kuma fafutikar da duniya ke yi na yaki da cin zarafi ta hanyar tabbatar da adalci.

Makasudin kafa kotun shi ne domin a tuhumi masu irin wannan laifuka da nufin zamewa darasi ga na baya ta yadda za a kauce wa faruwar irin wadannan laifuka.

Kotun ita ce mataki na karshe da za a iya bi, kuma ba an yi ta ne domin maye gurbin kotuna na cikin gida ba, sai dai domin ta taimaka musu.

An samar da kotun ne daga yarjejeniyar da aka cimma tsakanin kasashen duniya, wadda ake kira ‘Rome Statute.

Ita ce kotu ta farko ta duniya da aka kirkira domin hukunta manyan laifuka.

Kotun ICC na son ganin kasashe su amince da ita, domin samun karfin yaki da cin zarafi da kuma kare faruwar hakan a gaba.

Yanzu haka kotun tana da ma’aikata sama da 900 daga kimanin kasashe 100 na duniya.

Kotun na amfani da harsuna shida a hukumance, wato Ingilishi da Faransanci da Larabci da yaren China da na Rasha da kuma Sifaniyanci.

Kotun ta ce ta bayar da sammacin kame 61 ta hanayar hadin kai da kasashen duniya, kamar yadda ta wallafa a shafinta na intanet.

Haka nan ta samu nasarar tsare mutane 22 wadanda ta gurfanar a gabanta.

Har yanzu akwai mutane 30 wadanda ba ta samu damar kamawa ba, inda ta yi watsi da tuhume-tuhume kan mutum 8 sanadiyyar mutuwa.

Daga shekara ta 2002, alkalan kotun sun bayar da sammacin kama mutum tara domin gurfana a gabansu.

Haka nan sun samu nasarar kama mutum 11 da laifi yayin da suka wanke mutum 4.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Nijar
ShareTweetSendShare
Previous Post

Daga Kallon Fina-finan Indiya Na Samu Sha’awar Fadawa Kannywood – Kamalu Mijinyawa

Next Post

Majalisa Ta Daƙile PENGASSAN Akan Shirin Daina Kai Wa Matatar Ɗangote Gas Da Ɗanyen Mai

Related

Majalisa Ta Daƙile PENGASSAN Akan Shirin Daina Kai Wa Matatar Ɗangote Gas Da Ɗanyen Mai
Manyan Labarai

Majalisa Ta Daƙile PENGASSAN Akan Shirin Daina Kai Wa Matatar Ɗangote Gas Da Ɗanyen Mai

2 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Matatar Dangote Ta Dawo Sayar Da Man Fetur A KuÉ—in Naira

12 hours ago
Wannan Bishiya Ta Bayyana Sirrin Ci Gaban Jihar Xinjiang
Ra'ayi Riga

Wannan Bishiya Ta Bayyana Sirrin Ci Gaban Jihar Xinjiang

17 hours ago
Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu
Rahotonni

Masana Sun Dora Alhakin Rashin Cika Alkawuran ‘Yan Siyasa Kan Jam’iyyu

19 hours ago
Ana Hasashen Tashin Fetur Idan Matatar Dangote Ta Daina Karɓar Naira
Manyan Labarai

Ana Hasashen Tashin Fetur Idan Matatar Dangote Ta Daina Karɓar Naira

19 hours ago
Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba
Rahotonni

Rashin Aikin Yi: A Halin Yanzu Masu Digiri Na Sayar Da Fiya Wata Da Aikin Achaba

22 hours ago
Next Post
Majalisa Ta Daƙile PENGASSAN Akan Shirin Daina Kai Wa Matatar Ɗangote Gas Da Ɗanyen Mai

Majalisa Ta Daƙile PENGASSAN Akan Shirin Daina Kai Wa Matatar Ɗangote Gas Da Ɗanyen Mai

LABARAI MASU NASABA

Yaushe Za Ta Kare Wa Haaland?

Yaushe Za Ta Kare Wa Haaland?

September 28, 2025
Majalisa Ta Daƙile PENGASSAN Akan Shirin Daina Kai Wa Matatar Ɗangote Gas Da Ɗanyen Mai

Majalisa Ta Daƙile PENGASSAN Akan Shirin Daina Kai Wa Matatar Ɗangote Gas Da Ɗanyen Mai

September 28, 2025
Abin Da Ya Sa Nijar Da Mali Da Burkina Faso Suka Fice Daga Kotun Duniya Ta ICC

Abin Da Ya Sa Nijar Da Mali Da Burkina Faso Suka Fice Daga Kotun Duniya Ta ICC

September 28, 2025
Daga Kallon Fina-finan Indiya Na Samu Sha’awar Fadawa Kannywood – Kamalu Mijinyawa

Daga Kallon Fina-finan Indiya Na Samu Sha’awar Fadawa Kannywood – Kamalu Mijinyawa

September 28, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Matatar Dangote Ta Dawo Sayar Da Man Fetur A KuÉ—in Naira

September 27, 2025
Shugaban Cuba Ya Yi Bayani Kan Nazarin Fasahohin Sin A Fannoni Shida

Shugaban Cuba Ya Yi Bayani Kan Nazarin Fasahohin Sin A Fannoni Shida

September 27, 2025
Bukatar Mutane Su Kula Da Warin Jikinsu

Bukatar Mutane Su Kula Da Warin Jikinsu

September 27, 2025
Me Ya Sa Kamfanonin Jamus Fiye Da 560 Suka Zabi Wani Gari A Kasar Sin Don Gudanar Da Harkokinsu?

Me Ya Sa Kamfanonin Jamus Fiye Da 560 Suka Zabi Wani Gari A Kasar Sin Don Gudanar Da Harkokinsu?

September 27, 2025
Matsalar Tasgadewar Kashin Baya

Matsalar Tasgadewar Kashin Baya

September 27, 2025
Firaministan Sin: Adalci Shi Ne Abu Mafi Daraja A Wurin Kasashen Duniya 

Firaministan Sin: Adalci Shi Ne Abu Mafi Daraja A Wurin Kasashen Duniya 

September 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.