ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Nijar Da Mali Da Burkina Faso Suka Fice Daga Kotun Duniya Ta ICC

by Rabi'u Ali Indabawa
9 months ago
Nijar

Kasashen yankin Afirka ta yamma uku, Jamhuriyar Nijar da Mali da kuma Burkina Faso sun sanar da ficewar su daga kotun hukunta manyan laifuka ta ICC.

Kasashen sun bayyana cewa matakin nasu zai fara aiki ne nan take.

  • Matatar Dangote Ta Dawo Sayar Da Man Fetur A Kuɗin Naira
  • Me Ya Sa Kamfanonin Jamus Fiye Da 560 Suka Zabi Wani Gari A Kasar Sin Don Gudanar Da Harkokinsu?

A cikin wata sanarwar hadin gwiwa, shugabannin sun zargi kotun da zamewa “‘‘yar koren masu mulkin mallaka” wadda take “nuna son zuciya wajen yin hukunci.”

ADVERTISEMENT

Sanarwar wadda shugabannin kasashen suka fitar ta kuma zargi Kotun Hukunta Manyan Laifukan ta duniya da hukunta mutane daga kasashe marasa karfi, kuma ta nuna cewa “ta gaza” wajen hukunta laufuka mafi muni da ake tafkawa a doron kasa.

Wannan dai daya ne daga cikin matakan da kasashen uku suka dauka a baya-bayan nan bayan ficewarsu daga kungiyar hadin kan yammacin Afirka ta Ecowas, da kuma kafa kungiyar kasashen Sahle, wato AES.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

A shekarar 2003 ne aka kafa kotun ta ICC wadda aka dorawa alhakin hukunta laifukan da suka shafi kisan kare dangi da cin zarafin bil’Adama da laifukan yaki kuma tun lokacin da fara aiki kotun ta ICC ta saurari kararraki 33

Masu sukar kotun ciki har da shugaban kasar Ruwanda Paul Kagame sun zargi kotun da nuna son zuciya ko rashin adalci saboda ta fai maida hanakli kan kasashen Afrika. Sai dai magoya bayan kotun sun ce rashin tasirin fannin shariar kasashen Afrika ne ya sa mutane ko gwamnatoci ke neman adalci a kotun ta ICC

kasashen yannkin Sahel uku wadanda a halin yanzu ke fama da rashin tsaro sakamakon hare-haren mayaka masu ikirarnin jihadi sun yanke alaka da wasu kasashen yamma da suka hada Faransa inda suka kulla kawance da Rasha domin samun tallafin soji da kuma inganta cinikayya tsakaninsu.

Kasashen 33 daga cikin 54 mambobi ne a kotun ta ICC kuma ta ta fara bincike a wasu kasashen Afrika da suka gada jamhuriyat tsakiyar afrika da jamhuriyar dimokradiyar Kongo da Kenya da Libya da kuma Mali sauran sun hada da Sudan da Uganda da kuma Iboyry cost Yarjebiyar kafa Yarjejeniyar da ta kafa kotun ta bai wa mambobinta damar janyewa, sai dai matakin zai fara aiki ne bayan shekara guda daga lokacin sanarwar.

A shekarar 2017, Burundi ta zama kasa ta farko kuma daya tilo daga Afirka da ta yi nasarar ficewa daga kotun ta ICC.

 

Mece ce kotun hukunta manyan laifuka, kuma mene ne aikinta?

Babban aikin kotun hukunta manayan laifuka shi ne gurfanarwa da kuma hukunta mutanen da ake zargi da aikata kisan kiyashi, da laifukan yaki da kuma sauran laifuakan cin zarafin bil’adama.

Haka nan kotun takan iya yin bincike tare da gurfanar da mutanen da ake zargi da aikata munanan laifuka da suka zamo abin damuwa tsakanin kasashen duniya.

Kotun takan kuma fafutikar da duniya ke yi na yaki da cin zarafi ta hanyar tabbatar da adalci.

Makasudin kafa kotun shi ne domin a tuhumi masu irin wannan laifuka da nufin zamewa darasi ga na baya ta yadda za a kauce wa faruwar irin wadannan laifuka.

Kotun ita ce mataki na karshe da za a iya bi, kuma ba an yi ta ne domin maye gurbin kotuna na cikin gida ba, sai dai domin ta taimaka musu.

An samar da kotun ne daga yarjejeniyar da aka cimma tsakanin kasashen duniya, wadda ake kira ‘Rome Statute.

Ita ce kotu ta farko ta duniya da aka kirkira domin hukunta manyan laifuka.

Kotun ICC na son ganin kasashe su amince da ita, domin samun karfin yaki da cin zarafi da kuma kare faruwar hakan a gaba.

Yanzu haka kotun tana da ma’aikata sama da 900 daga kimanin kasashe 100 na duniya.

Kotun na amfani da harsuna shida a hukumance, wato Ingilishi da Faransanci da Larabci da yaren China da na Rasha da kuma Sifaniyanci.

Kotun ta ce ta bayar da sammacin kame 61 ta hanayar hadin kai da kasashen duniya, kamar yadda ta wallafa a shafinta na intanet.

Haka nan ta samu nasarar tsare mutane 22 wadanda ta gurfanar a gabanta.

Har yanzu akwai mutane 30 wadanda ba ta samu damar kamawa ba, inda ta yi watsi da tuhume-tuhume kan mutum 8 sanadiyyar mutuwa.

Daga shekara ta 2002, alkalan kotun sun bayar da sammacin kama mutum tara domin gurfana a gabansu.

Haka nan sun samu nasarar kama mutum 11 da laifi yayin da suka wanke mutum 4.

Nijar
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Next Post
Majalisa Ta Daƙile PENGASSAN Akan Shirin Daina Kai Wa Matatar Ɗangote Gas Da Ɗanyen Mai

Majalisa Ta Daƙile PENGASSAN Akan Shirin Daina Kai Wa Matatar Ɗangote Gas Da Ɗanyen Mai

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.