ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, September 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Nijar Da Mali Da Burkina Faso Suka Fice Daga Kotun Duniya Ta ICC

by Rabi'u Ali Indabawa
12 months ago
Nijar

Kasashen yankin Afirka ta yamma uku, Jamhuriyar Nijar da Mali da kuma Burkina Faso sun sanar da ficewar su daga kotun hukunta manyan laifuka ta ICC.

Kasashen sun bayyana cewa matakin nasu zai fara aiki ne nan take.

  • Matatar Dangote Ta Dawo Sayar Da Man Fetur A Kuɗin Naira
  • Me Ya Sa Kamfanonin Jamus Fiye Da 560 Suka Zabi Wani Gari A Kasar Sin Don Gudanar Da Harkokinsu?

A cikin wata sanarwar hadin gwiwa, shugabannin sun zargi kotun da zamewa “‘‘yar koren masu mulkin mallaka” wadda take “nuna son zuciya wajen yin hukunci.”

ADVERTISEMENT

Sanarwar wadda shugabannin kasashen suka fitar ta kuma zargi Kotun Hukunta Manyan Laifukan ta duniya da hukunta mutane daga kasashe marasa karfi, kuma ta nuna cewa “ta gaza” wajen hukunta laufuka mafi muni da ake tafkawa a doron kasa.

Wannan dai daya ne daga cikin matakan da kasashen uku suka dauka a baya-bayan nan bayan ficewarsu daga kungiyar hadin kan yammacin Afirka ta Ecowas, da kuma kafa kungiyar kasashen Sahle, wato AES.

LABARAI MASU NASABA

Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

Makiyaya Sun Yi Asarar Shanu 200,000 Ta Dalilin Rikice-Rikice – MACBAN

A shekarar 2003 ne aka kafa kotun ta ICC wadda aka dorawa alhakin hukunta laifukan da suka shafi kisan kare dangi da cin zarafin bil’Adama da laifukan yaki kuma tun lokacin da fara aiki kotun ta ICC ta saurari kararraki 33

Masu sukar kotun ciki har da shugaban kasar Ruwanda Paul Kagame sun zargi kotun da nuna son zuciya ko rashin adalci saboda ta fai maida hanakli kan kasashen Afrika. Sai dai magoya bayan kotun sun ce rashin tasirin fannin shariar kasashen Afrika ne ya sa mutane ko gwamnatoci ke neman adalci a kotun ta ICC

kasashen yannkin Sahel uku wadanda a halin yanzu ke fama da rashin tsaro sakamakon hare-haren mayaka masu ikirarnin jihadi sun yanke alaka da wasu kasashen yamma da suka hada Faransa inda suka kulla kawance da Rasha domin samun tallafin soji da kuma inganta cinikayya tsakaninsu.

Kasashen 33 daga cikin 54 mambobi ne a kotun ta ICC kuma ta ta fara bincike a wasu kasashen Afrika da suka gada jamhuriyat tsakiyar afrika da jamhuriyar dimokradiyar Kongo da Kenya da Libya da kuma Mali sauran sun hada da Sudan da Uganda da kuma Iboyry cost Yarjebiyar kafa Yarjejeniyar da ta kafa kotun ta bai wa mambobinta damar janyewa, sai dai matakin zai fara aiki ne bayan shekara guda daga lokacin sanarwar.

A shekarar 2017, Burundi ta zama kasa ta farko kuma daya tilo daga Afirka da ta yi nasarar ficewa daga kotun ta ICC.

 

Mece ce kotun hukunta manyan laifuka, kuma mene ne aikinta?

Babban aikin kotun hukunta manayan laifuka shi ne gurfanarwa da kuma hukunta mutanen da ake zargi da aikata kisan kiyashi, da laifukan yaki da kuma sauran laifuakan cin zarafin bil’adama.

Haka nan kotun takan iya yin bincike tare da gurfanar da mutanen da ake zargi da aikata munanan laifuka da suka zamo abin damuwa tsakanin kasashen duniya.

Kotun takan kuma fafutikar da duniya ke yi na yaki da cin zarafi ta hanyar tabbatar da adalci.

Makasudin kafa kotun shi ne domin a tuhumi masu irin wannan laifuka da nufin zamewa darasi ga na baya ta yadda za a kauce wa faruwar irin wadannan laifuka.

Kotun ita ce mataki na karshe da za a iya bi, kuma ba an yi ta ne domin maye gurbin kotuna na cikin gida ba, sai dai domin ta taimaka musu.

An samar da kotun ne daga yarjejeniyar da aka cimma tsakanin kasashen duniya, wadda ake kira ‘Rome Statute.

Ita ce kotu ta farko ta duniya da aka kirkira domin hukunta manyan laifuka.

Kotun ICC na son ganin kasashe su amince da ita, domin samun karfin yaki da cin zarafi da kuma kare faruwar hakan a gaba.

Yanzu haka kotun tana da ma’aikata sama da 900 daga kimanin kasashe 100 na duniya.

Kotun na amfani da harsuna shida a hukumance, wato Ingilishi da Faransanci da Larabci da yaren China da na Rasha da kuma Sifaniyanci.

Kotun ta ce ta bayar da sammacin kame 61 ta hanayar hadin kai da kasashen duniya, kamar yadda ta wallafa a shafinta na intanet.

Haka nan ta samu nasarar tsare mutane 22 wadanda ta gurfanar a gabanta.

Har yanzu akwai mutane 30 wadanda ba ta samu damar kamawa ba, inda ta yi watsi da tuhume-tuhume kan mutum 8 sanadiyyar mutuwa.

Daga shekara ta 2002, alkalan kotun sun bayar da sammacin kama mutum tara domin gurfana a gabansu.

Haka nan sun samu nasarar kama mutum 11 da laifi yayin da suka wanke mutum 4.

Nijar
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas

MASU ALAKA

Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom
Labarai

Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

September 13, 2026
Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom
Labarai

Makiyaya Sun Yi Asarar Shanu 200,000 Ta Dalilin Rikice-Rikice – MACBAN

September 13, 2026
Nijar
Labarai

Malamai Da Limamai 3,000 Sun Yi Addu’ar Zaman Lafiya Da Nasarar Tinubu A 2027

September 13, 2026
Next Post
Majalisa Ta Daƙile PENGASSAN Akan Shirin Daina Kai Wa Matatar Ɗangote Gas Da Ɗanyen Mai

Majalisa Ta Daƙile PENGASSAN Akan Shirin Daina Kai Wa Matatar Ɗangote Gas Da Ɗanyen Mai

LABARAI MASU NASABA

Manchester Derby: City Ta Nunawa United Kwanji A Old Trafford

Manchester Derby: City Ta Nunawa United Kwanji A Old Trafford

September 13, 2026
Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

September 13, 2026
Ka Kyale Ni Nayi Wa Mutanen Binuwai Aiki – Gwamna Alia Ga Ortom

Makiyaya Sun Yi Asarar Shanu 200,000 Ta Dalilin Rikice-Rikice – MACBAN

September 13, 2026
Nijar

Farashin Man Fetur Ya Sake Tashi A Abuja

September 13, 2026
Shugabannin BRICS Sun Amince Da Sanarwar Hadin Gwiwa A Taron Koli Na New Delhi

Shugabannin BRICS Sun Amince Da Sanarwar Hadin Gwiwa A Taron Koli Na New Delhi

September 13, 2026
Nijar

Malamai Da Limamai 3,000 Sun Yi Addu’ar Zaman Lafiya Da Nasarar Tinubu A 2027

September 13, 2026
An Samu Babban Sakamako Kan Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa Na Duniya

An Samu Babban Sakamako Kan Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa Na Duniya

September 13, 2026
Ministan Kimiyya Na Afirka Ta Kudu Ya Yi Kiran Zurfafa Hadin Gwiwar Kimiyya Da Fasaha Da Sin

Ministan Kimiyya Na Afirka Ta Kudu Ya Yi Kiran Zurfafa Hadin Gwiwar Kimiyya Da Fasaha Da Sin

September 13, 2026
Nijar

An Gudanar Da Sallar Zana’idar Tsohon Gwamnan Gongola

September 13, 2026
Yajin Aikin ASUU: Malaman Jami’ar Jihar Kaduna Sun Bijirewa El-rufa’i

Gwamna Uba Sani Ya Amince Da Ƙarin Albashi Ga Ma’aikatan KASU

September 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.