• English
  • Business News
Friday, August 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Ya Sa Putin Ke Samun Karfin Iko Fiye Da Kowane Lokaci

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
in Labarai
0
Abin Da Ya Sa Putin Ke Samun Karfin Iko Fiye Da Kowane Lokaci

Russian presidential candidate and incumbent President Vladimir Putin speaks after polling stations closed, in Moscow, Russia, March 18, 2024. REUTERS/Maxim Shemetov

Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Cire Tallafin Mai Ya Taimaka Mana Wajen Aiwatar da Ayyuka, In Ji Gwamna Mbah

An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano

Shugaba Bladimir Putin ya lashe zabe karo na biyar, inda zai ci gaba da jagoranci har shekara ta 2030.

A jawabin da ya yi bayan samun nasara, ya ce nasararsa za ta sanya Rasha ta kara samun karfi da kuma yin tasiri.

  • Noman Gwanda Da Kasuwancinta A Saukake
  • Ku Yi Amanna Da Tinubu, Matsalolin Zu Su Zo Karshe, inji Ministan YaÉ—a Labarai

Ya lashe zaben ne da gagarumar nasara inda ya samu kashi 87 na kuri’un da aka kada, abin da ya zarce wanda ya samu a zaben da ya gabata na kashi 76.7 na kuri’un. Duk da cewa bai samu wata adawa mai karfi ba, fadar Kremlin ita ke iko da tsarin siyasar kasar, da kafafen yada labaru da kuma zabuka.

Shugabannin kasashen Yamma da dama sun yi Alla-wadai da zaben inda suka ayyana shi a matsayin mai rashin inganci, ciki har da shugaban kasar Ukraine Bolodymyr Zelensky, wanda ya kira Putin a matsayin mai mulkin kama karya wanda kuma giyar mulki ta buga, inda ya kara da cewa: “Zai iya yin komai domin ci gaba da zama a kan mulki.”

Putin, mai shekara 71, wanda ya fara shugabanci a ranar karshe ta shekarar 1999 – ya kasance shugaban kasar mafi dadewa kan mulki tun bayan Joseph Stalin, kuma a halin yanzu zai karya tarihin da mutumin mai mulkin kama-karya na tarayyar Sobiet ya kafa a baya.

Duk da cewa ‘yan Rasha na mutuwa a yakin da take yi da Ukraine, wanda ke shiga shekara ta uku da farawa, yayin kuma da Rasha take kara zama saniyar ware tsakanin kasashen Yamma, ga wasu dalilai da suka sa Putin ya ke da karfin iko da ba a taba gani a baya ba.

Girman tattalin arzikin Rasha

Duk da irin tarin takunkumi da aka kakaba wa Rasha bayan mamayar da ta yi a Ukraine, kasar ta bai wa masana tattalin arziki da dama mamaki ta hanyar zama kasar da tattalin arzikinta ke habaka cikin sauri a Turai.

“Tattalin arzikin na cikin yanayi mai kyau, dukkan abubuwa na tafiya yadda ya kamata, kuma hakan ya saka Putin zama sananne saboda ya sake nuna kansa a matsayin mutumin da ya bijire wa Yamma kan takunkumi da suka saka wa tattalin arzikin Rasha,” in ji wakilin BBC a bangaren kasuwanci, Aledey Kalmykob.

Maimakon faduwa kasa kamar yadda mutane da dama suka yi tsammani, tattalin arzikin Rasha ya karu da kashi 2.6, a cewar kiyasin Hukumar Ba Da Lamuni ta Duniya (IMF), duk da takunkuman Yamma, da suka hada da hana Rashar taba kudinta da ya kai Dala biliyan 300.

Sai dai wadannan takunkumai ba su yi aiki a fadin duniya ba. Wannan ya bai wa Rasha damar huldar kasuwanci da kasashen China, Indiya da kuma Brazil yayin da makwabta, ciki har da Kazakhstan da Armenia, na taimaka wa Rasha kauce wa takunkuman Yamma.

“Tattalin arzikin Rasha na da grima,” in ji Kalmykob, ya kara da cewa: “Za a dauki tsawon gomman shekaru kafin takunkumai ko barnar kudi su kai tattalin arzikin Rasha kasa kasa amma dai ba yanzu ba.”

“Rasha na samun kudi ta hanyar fitar da kayyaki waje kuma tana da damar sayar da duk abin da take so,” a cewar Kalmykob. “takunkumi kan man fetur na je ka na yi ka ne, sai dai babu takunkumi kan iskar gas da kuma nukiliya daga Tarayyar Turai saboda suna cikin wadanda ke sayen abubuwan daga Rasha.”

Dakta Schulmann ya ce duk da cewa farashin kayyaki ya ninka har sau hudu ba kamar a baya ba, a shirye suke, wanda ta ce yana da muhimmancin gaske.

“An san Rasha da kara farashin kayayyaki. Fargabar da muke da ita ba wai ta hauhawar farashi ba ne, sai dai illa gibi.

Kalmykob ya amince cewa: “Abu daya shi ne farfagandar Putin na iya yin tasiri matuka.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Arsenal Za Ta Iya Kai Bantenta Kuwa?

Next Post

Ɗaliban Kuriga 137 Muka Yi Nasarar Kuɓutarwa A Zamfara, Ba Ɗalibai 287 Ba— Sojoji

Related

Cire Tallafin Mai Ya Taimaka Mana Wajen Aiwatar da Ayyuka, In Ji Gwamna Mbah
Labarai

Cire Tallafin Mai Ya Taimaka Mana Wajen Aiwatar da Ayyuka, In Ji Gwamna Mbah

46 minutes ago
An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano
Labarai

An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano

1 hour ago
Shugaba Tinubu Ya NaÉ—a Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya NaÉ—a Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci

3 hours ago
Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda
Rahotonni

Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

3 hours ago
Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

4 hours ago
Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara
Manyan Labarai

Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara

5 hours ago
Next Post
Ɗaliban Kuriga 137 Muka Yi Nasarar Kuɓutarwa A Zamfara, Ba Ɗalibai 287 Ba— Sojoji

Ɗaliban Kuriga 137 Muka Yi Nasarar Kuɓutarwa A Zamfara, Ba Ɗalibai 287 Ba— Sojoji

LABARAI MASU NASABA

Cire Tallafin Mai Ya Taimaka Mana Wajen Aiwatar da Ayyuka, In Ji Gwamna Mbah

Cire Tallafin Mai Ya Taimaka Mana Wajen Aiwatar da Ayyuka, In Ji Gwamna Mbah

August 15, 2025
NPA Ta Fito Da Sabuwar Doka Kan Kayan Da Ake Ajiyewa A Tashoshinta

NPA Ta Fito Da Sabuwar Doka Kan Kayan Da Ake Ajiyewa A Tashoshinta

August 15, 2025
An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano

An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano

August 15, 2025
Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata

Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata

August 15, 2025
Shugaba Tinubu Ya NaÉ—a Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci

Shugaba Tinubu Ya NaÉ—a Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci

August 15, 2025
Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

August 15, 2025
Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

August 15, 2025
Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara

Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara

August 15, 2025
Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

August 14, 2025
NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata

NLC Ta Baiwa Gwamnati Kwanaki 7 Don Magance Badaƙalar Satar Kuɗin Ma’aikata

August 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.