• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Ba A Sani Ba Game Da Sabon Harin Bam Na Kaduna

byShehu Yahaya and Sulaiman
1 year ago
Harin Bam
  • Yadda Abin Ya Faru –Ganau
  • Tabbas ‘Yan Ta’adda Muka Farmaka –NAF

Al’ummar Kauyen Jika da Kolo da ke garin Yadin Kidandan a karamar hukumar Giwa da ke Jihar Kaduna na ci gaba da zaman dar-dar bisa zargin kai musu hari da jiragen sojin saman Nijeriya ya kai musu a makon da ya gabata.

 

Al’ummar garin sun zargi sojojin sama da jefa musu bam yayin da suke gudanar da sallar Juma’a a cikin masallaci da kuma kasuwa, wanda hakan ya yi sanadiyyar mutuwar mutum 23.

  • Tsadar Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Za Su Kaɗa Ƙuri’ar Kawo Canji Na Gaskiya A 2027 – Kwankwaso
  • Gwamna Sani Zai Kaddamar Da Cibiyar Kula Da Cutar Kansa Mai Gadaje 300 A Kaduna – Kwamishina

Harin bam din ya haifar da cece-kuce tsakanin al’ummar garin da runduna sojin saman Nijeriya, inda mutanan kauyen suke zargin sojoji sun kai harin mai uwa da wabi.

 

LABARAI MASU NASABA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Sai dai a nata, bangaren rundunar sojin saman Nijeriya ta musanta wanna zargi, ta kuma bayyana cewa harin da ta kai ya tafi kai tsaye ne ga sansanin babban dan bindiga mai suna Kadade Gurgu, wanda na hannun daman dan ta’adda Dogo Gide ne.

 

A wata ziyara da wakilinmu ya kai a yankin karamar hukumar Giwa, wasu mazauna garin sun bayyana cewa akwai fararen hula da harin sojojin ya shafa.

 

Haka zalika, sun kamanta harin da sojojin suka kai da wanda aka kai a baya a garin Tudun Biri, wanda ya yi sanadiyyar rasa ran masu Mauludi kimamnin guda 100 a watan Disamban 2023.

 

Wani magidancin dan asalin garin Kidandan, ya bayyana wa wakilinmu yadda abin ya faru, yana mai cewa, “Bisa batun tsaro ba zan iya bayyana sunana ba, amma dai ni dan asalin garin Kidandan ne kuma a nan aka haife, sannan a nan nake rayuwa, bisa matsalar tsaro ya sanya muke zuwa garin jifa-jifa.

 

“Yadin Kidandan gari ne wanda ya zama sansanin ‘yan ta’adda. Wanda yanzu shiga garin idan kai ba dan gari ba ne ba ya shiguwa. Ranar Juma’ar da ta gabata, wani jirgi ya kai hari har ya yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama. Amma batun gaskiya shi ne, har yanzu babu wani wanda zai iya tantance cewa wadanda suka mutu a harin ‘yan garin ne kadai babu ‘yan ta’adda a ciki, saboda gari ne wanda yake cakude da mutanan kirki da ‘yan ta’adda.”

 

Wani mazaunin garin Jika da Kolo da ke zaune a garin Gwargwaji a Zariya ya shaida cewa, “Yawancinmu har yanzu muna zaune a kusa da kauyen, saboda ba mu da wani wurin da za mu koma. A nan aka haifi kakanninmu.

 

Mun rasa ‘yan uwanmu da yawa, ciki har da yara marasa laifi.

 

“Kuma batun cewa harin ya rusa da masallaci ba haka ba ba ne. An dai kashe mutane amma harin bai taba masallaci ba.”

 

Sai dai wani bincike da LEADERSHIP HAUSA ta gudanar ya nuna cewa masallacin da al’ummar garin na Jika da Kolo suke zargin sajojin sun kai hari, dan siyasa daga Jihar Kano, Alhaji Ibrahim Ali Amin “Little”, ya gina musu. Wanda yake kusa da wat babbar gonarsa da ke yankin domin gudanar da sallar Juma’a.

 

Majiyarmu ta shaida mana cewa shekaru biyu baya, shi kansa dan siyasar ya tsallake rijiya da baya daga hannun ‘yan ta’adda, inda aka harbe shi a hannu, lamarin da sanya ya dakatar da zuwa gonar bisa matsalar rashin tsaro.

 

A wata sanarwar da rundunar sojan sama ta fitar ta hannun daraktan yada labaranta, Kaftin Kabiru Ali, ya jaddada cewa ba su Kai hari a masallaci ba, kuma duk wani bayani zai zo ne bayan da rundunar ta kammala bincike.

 

Rundunar ta kara da cewa ta kashe ‘yan ta’adda da dama yayin harin da ta kai, amma babu masallaci a wurin da jiragen suka kai harin.

 

A wata zantawa da ya yi da wakilinmu, Kansilar Mazabar Kidandan, Abdullahi Ismail, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce kauyen Jika da Kolo ya zama sansanin ‘yan ta’adda da suke cin kasuwarsu babu babbaka.

 

Majiyarmu ta tabbatar da cewa an yi jana’izar mutane da suka ransu su 23.

 

Wakilinmu ya yi kokarin jin ta bakin kwamshinan harkokin tsaro na Jihar Kaduna, Samuel Aruwan kan lamarin, inda ya kira wayarsa har sau uku bai dauka ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Next Post
NPA Ta Samar Da Sabon Tsari Don Bunksa Tasoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

NPA Ta Samar Da Sabon Tsari Don Bunksa Tasoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version