ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Sani Zai Kaddamar Da Cibiyar Kula Da Cutar Kansa Mai Gadaje 300 A Kaduna – Kwamishina

by Sulaiman
2 years ago
Sani

Gwamna Uba Sani ya yi alkawarin kammalawa tare da kaddamar da wani asibitin kwararru mai gadaje 300 wanda aka tanada musamman don kula da masu cutar kansa a Millennium city, da ke Kaduna a karshen shekarar 2024.

 

Wannan aikin asibitin wanda tsohon mataimakin shugaban kasa, Namadi Sambo ya kaddamar, ya samu tallafin dala miliyan 148 daga bankin cigaban Musulunci (IDB) da nufin samar da cikakkiyar cibiyar kiwon lafiya ga al’ummar jihar Kaduna.

ADVERTISEMENT
  • Zaɓen Ƙananan Hukumomi: Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Yaƙin Neman Zaɓen APC
  • Sanatocin Arewa 12 Da Suka Gaza Gabatar Da Ƙudiri A Watanni 15

Duk da kokarin da gwamnatocin baya da suka hada da na Patrick Yakowa, Mukhtar Ramadan Yero, da Nasir Ahmed El-Rufai suka yi, har yanzu aikin bai kammala ba.

 

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Da take magana, kwamishiniyar lafiya ta jihar Hajia Umma K. Ahmed a wani taron manema labarai a ranar Laraba, da take bayyana irin nasarorin da gwamnatin Sanata uba Sani ta samu a fannin kiwon lafiya, ta ce, Gwamna Sani ya ce: “A cikin zango na karshe na shekarar 2024, zai gayyace ‘yan jarida domin kaddamar da kammala ginin wannan katafariyar cibiyar kiwon lafiya ta zamani.

 

“Kaddamar da wannan cibiya ta zamani, za ta kawo sauyi tare da gyara harkokin kiwon lafiya na Jiha tare da rage yawan fita zuwa kasashen ketare don neman magani, domin asibitin mai gadaje 300 yana da sashen binciken cututtukan daji da kuma magance cutar. ”

 

Gwamnan ya ce, tsaren-tsaren inganta kiwon lafiya ya bada fifiko matuka wajen samar da kayan aiki a dukkan matakan kiwon lafiya da suka hada da na farko, matsakaita da manya a jihar, inda ya ce, gwamnati na inganta manyan asibitoci 9, inda aka zabo uku-uku daga cikin shiyyoyi Uku da ke jihar.

 

“Asibitocin sun hada da Asibitin Maigana, Asibitin Rigasa, Asibitin Gwantu, Asibitin Ikara, Asibitin Patrick Ibrahim Yakowa, da Asibitin Giwa.”

 

Sauran sun hada da “Sabon Asibitin Tunawa da Dabo Lere, Asibitin Sabon Tasha, da Asibitin Kachia”. in ji ta.

 

Wadannan Asibitocin, a halin yanzu suna cikin matakai daban-daban na sake ginawa, sake fasali, da kuma samar da kayan aiki a matsayin wani bangare na shirin Gwamnati na inganta cibiyoyin kiwon lafiya.

 

Gwamnan ya kara da cewa, ana kokarin samar da ababen more rayuwa ne domin ganin an samu sauyi a kowane mataki domin samar da ingantacciyar kulawa ga al’ummar jihar Kaduna.

 

Hajiya Umma ta jaddada cewa: “Tun da ya hau kan karagar mulki a ranar 29 ga Mayu, 2023, Gwamna Uba Sani ya nuna jajircewarsa na kawo sauyi a fannin kiwon lafiya.”

Sani
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
  • Sulaiman
    Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
  • Sulaiman
    Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci
  • Sulaiman
    Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

MASU ALAKA

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili
Labarai

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya
Rahotonni

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
Sin Ta Bukaci Kwamitin Sulhun MDD Da Ya Ingiza Sassauta Rikicin Lebanon Da Isra’ila

Sin Ta Bukaci Kwamitin Sulhun MDD Da Ya Ingiza Sassauta Rikicin Lebanon Da Isra’ila

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.