• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Ya Kamata A Sani Game Da Dannau

by Sani Anwar
2 years ago

A likitance ana kiran Dannau da (sleep paralysis), a gargajiyance kuma ana kiran sa da Aljanin dare. A nan wani yanayi da mutum yake samun kansa a yayin bacci ko a farke, ta hanyar da mutum yana ji yana gani ya kasa yin numfashi ko motsi. A irin wannan lokaci, wasu har gane-gane suke yi barkatai; shi ya sa ake alakanta al’amarin da shedanu ko Mayu da sauran makamantansu.

Bugu da kari, duk a cikin mutum goma; akalla ana samun mutum hudu da ke shiga cikin irin wannan yanayi lokaci zuwa lokaci, sannan duk wanda ya samu kansa a wannan yanayi, ba ya wuce wasu ‘yan dakiku ko mintuna kafin ya samu kansa ko ya dawo hayyacinsa.

  • Hisbah Ta Yi Wa Mutum 4,000 Rajista Da Ke Son Gwamnatin Kano Ta Aurar Da Su
  • Duk Da Hukuncin Kotu, Gwamna Yusuf Ya Amince Da Kashe Naira Biliyan 3 Kan Ayyuka

Har ila yau, wannan yanayi da yake da alaka da Dannau, kamar yadda likitoci suka bayyana, yana faruwa ne sakamakon yadda baccin kowane Dan Adam ya rabu zuwa gida biyu, wanda a turance ake kira da ‘REM sleep’ da kuma ‘Non REM sleep’, ma’ana matakin bacci na farko da kuma na biyu. A matakin farko ne mutum yake samun damar yin mafarki, a inda kwakwalwa ke aike wa da gabobin Dan Adam da sako ta yadda idan yana yin bacci zai iya motsawa duk inda yake so a kuma duk lokacin da ya gama.

Saboda haka, a wannan lokaci na matakin bacci na farko (REM sleep), kwakwalwar na kashe mukunnin da ke kai wannan sako zuwa gabban mutum don gudun ka da ya yi hanzari ko gaggawar tashi ta kai shi ga jin ciwo ko rauni. Don haka, idan mutum ya zo tashi daga bacci, ya kamata kwakwalwar tasa ta gane cewa ya zo tashi, ta koma ta sake kunna makunnin wadannan gabbai nasa kafin ya kai ga tashin, amma a wasu lokutan sai a samu akasin haka kwakwalwar ta ki kunna wannan makunni, daga nan sai a samu akasi mutum ya kasa motsi ko yin numfashi har zuwa wasu dakikai ko ‘yan mintina kafin kwakwalwar ta gano cewa ta yi kuskure ba ta kunna ba, ta dawo ta sake kunna wannan mukunni.

Haka nan, a gargajiyance ana alakanta wannan matsala ta Dannau da Aljanin dare ko sharrin Mayu. Duk da cewa, yanayin da ake shiga kamar yadda a likitance aka bayyana iri daya ne, ta yadda mutum zai ji ya kasa numfashi ko motsi har zuwa wasu ‘yan dakikai ko mintina. Sannan, sau tari mutum ya kan ji jikinsa ya yi nauyi kamar an dora masa wani katon dutse ko an daddaure shi takamau; a cikin baccinsa ko ido biyu, wani lokacin ma wasu kan ce har shedanun ake gani ido kuru-kuru.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

Wasu kuma na danganta wannan al’amari kai tsaye ga matsalar Mayu, ta yadda a cewarsu; ana ganin Mayen a daidai wannan lokaci, ko ya zo shi kadai ko kuma tare da wasu abokai ko ‘yan’uwansa; musamman idan ya kasance yana da wata matsala ko takun saka da wani. Ko kuma ya yi basaja ta hanyar zuwa a kamannin wani dan’uwanka ko wanda ka sani don ya hada ka gaba da shi ko gudun ka da ka ramfo shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka
Kiwon Lafiya

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025
Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha
Kiwon Lafiya

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025
Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa
Kiwon Lafiya

Wasu Daga Cikin Muhimman Alamomin Ciwon Kansa

October 11, 2025
Next Post
’Yan Wasan Kasar Sin Sun Zarce Tsammani A Hangzhou 

’Yan Wasan Kasar Sin Sun Zarce Tsammani A Hangzhou 

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

Shugabannin DSS Sun Gana A Kaduna, Sun Tattauna Matsalar Tsaron Arewa Maso Yamma

November 7, 2025
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Karu Da Kashi 3.6 Cikin Dari A Watanni 10 Na Farkon Shekarar 2025

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

Kasar Sin Za Ta Dage Dakatar Da Shigo Da Waken Soya A Kan Kamfanonin Amurka Uku 

November 7, 2025
Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

An Yi Kira Da A Zurfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Kasashen Afirka Don Bunkasa Masana’antu A Sassan Afirka

November 7, 2025
APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Yadda PDP Ta Yi Asarar Kudancin Kaduna

November 7, 2025
Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Ya Halarci Taron COP30 A Brazil

November 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.