ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Ya Kamata A Sani Game Da Dannau

by Sani Anwar
3 years ago

A likitance ana kiran Dannau da (sleep paralysis), a gargajiyance kuma ana kiran sa da Aljanin dare. A nan wani yanayi da mutum yake samun kansa a yayin bacci ko a farke, ta hanyar da mutum yana ji yana gani ya kasa yin numfashi ko motsi. A irin wannan lokaci, wasu har gane-gane suke yi barkatai; shi ya sa ake alakanta al’amarin da shedanu ko Mayu da sauran makamantansu.

Bugu da kari, duk a cikin mutum goma; akalla ana samun mutum hudu da ke shiga cikin irin wannan yanayi lokaci zuwa lokaci, sannan duk wanda ya samu kansa a wannan yanayi, ba ya wuce wasu ‘yan dakiku ko mintuna kafin ya samu kansa ko ya dawo hayyacinsa.

  • Hisbah Ta Yi Wa Mutum 4,000 Rajista Da Ke Son Gwamnatin Kano Ta Aurar Da Su
  • Duk Da Hukuncin Kotu, Gwamna Yusuf Ya Amince Da Kashe Naira Biliyan 3 Kan Ayyuka

Har ila yau, wannan yanayi da yake da alaka da Dannau, kamar yadda likitoci suka bayyana, yana faruwa ne sakamakon yadda baccin kowane Dan Adam ya rabu zuwa gida biyu, wanda a turance ake kira da ‘REM sleep’ da kuma ‘Non REM sleep’, ma’ana matakin bacci na farko da kuma na biyu. A matakin farko ne mutum yake samun damar yin mafarki, a inda kwakwalwa ke aike wa da gabobin Dan Adam da sako ta yadda idan yana yin bacci zai iya motsawa duk inda yake so a kuma duk lokacin da ya gama.

ADVERTISEMENT

Saboda haka, a wannan lokaci na matakin bacci na farko (REM sleep), kwakwalwar na kashe mukunnin da ke kai wannan sako zuwa gabban mutum don gudun ka da ya yi hanzari ko gaggawar tashi ta kai shi ga jin ciwo ko rauni. Don haka, idan mutum ya zo tashi daga bacci, ya kamata kwakwalwar tasa ta gane cewa ya zo tashi, ta koma ta sake kunna makunnin wadannan gabbai nasa kafin ya kai ga tashin, amma a wasu lokutan sai a samu akasin haka kwakwalwar ta ki kunna wannan makunni, daga nan sai a samu akasi mutum ya kasa motsi ko yin numfashi har zuwa wasu dakikai ko ‘yan mintina kafin kwakwalwar ta gano cewa ta yi kuskure ba ta kunna ba, ta dawo ta sake kunna wannan mukunni.

Haka nan, a gargajiyance ana alakanta wannan matsala ta Dannau da Aljanin dare ko sharrin Mayu. Duk da cewa, yanayin da ake shiga kamar yadda a likitance aka bayyana iri daya ne, ta yadda mutum zai ji ya kasa numfashi ko motsi har zuwa wasu ‘yan dakikai ko mintina. Sannan, sau tari mutum ya kan ji jikinsa ya yi nauyi kamar an dora masa wani katon dutse ko an daddaure shi takamau; a cikin baccinsa ko ido biyu, wani lokacin ma wasu kan ce har shedanun ake gani ido kuru-kuru.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida

Wasu kuma na danganta wannan al’amari kai tsaye ga matsalar Mayu, ta yadda a cewarsu; ana ganin Mayen a daidai wannan lokaci, ko ya zo shi kadai ko kuma tare da wasu abokai ko ‘yan’uwansa; musamman idan ya kasance yana da wata matsala ko takun saka da wani. Ko kuma ya yi basaja ta hanyar zuwa a kamannin wani dan’uwanka ko wanda ka sani don ya hada ka gaba da shi ko gudun ka da ka ramfo shi.

Dannau
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sojoji Sun Ceto Mutum 92 Tare Da Daƙile Harin Ƴan Ta’adda A Borno
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Uzodimma: Babu Dimokraɗiyya Idan Babu Hamayya
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Ministocin Da Suka Ajiye Muƙamansu Ba Su Samu Tikitin Takara Ba

MASU ALAKA

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir
Kiwon Lafiya

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

May 30, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Kiwon Lafiya

Alamomin Fara Ruɓewar Hannu Bayan Ɗorin Gida

May 23, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Yi Wa Mutane 6,842 Tiyata Kyauta A Kashi 17 Na Shirin Tallafin Lafiya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Yi Wa Mutane 6,842 Tiyata Kyauta A Kashi 17 Na Shirin Tallafin Lafiya

May 21, 2026
Next Post
’Yan Wasan Kasar Sin Sun Zarce Tsammani A Hangzhou 

’Yan Wasan Kasar Sin Sun Zarce Tsammani A Hangzhou 

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.