ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 27, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Ya Kamata A Sani Game Da Dannau

by Sani Anwar
3 years ago

A likitance ana kiran Dannau da (sleep paralysis), a gargajiyance kuma ana kiran sa da Aljanin dare. A nan wani yanayi da mutum yake samun kansa a yayin bacci ko a farke, ta hanyar da mutum yana ji yana gani ya kasa yin numfashi ko motsi. A irin wannan lokaci, wasu har gane-gane suke yi barkatai; shi ya sa ake alakanta al’amarin da shedanu ko Mayu da sauran makamantansu.

Bugu da kari, duk a cikin mutum goma; akalla ana samun mutum hudu da ke shiga cikin irin wannan yanayi lokaci zuwa lokaci, sannan duk wanda ya samu kansa a wannan yanayi, ba ya wuce wasu ‘yan dakiku ko mintuna kafin ya samu kansa ko ya dawo hayyacinsa.

  • Hisbah Ta Yi Wa Mutum 4,000 Rajista Da Ke Son Gwamnatin Kano Ta Aurar Da Su
  • Duk Da Hukuncin Kotu, Gwamna Yusuf Ya Amince Da Kashe Naira Biliyan 3 Kan Ayyuka

Har ila yau, wannan yanayi da yake da alaka da Dannau, kamar yadda likitoci suka bayyana, yana faruwa ne sakamakon yadda baccin kowane Dan Adam ya rabu zuwa gida biyu, wanda a turance ake kira da ‘REM sleep’ da kuma ‘Non REM sleep’, ma’ana matakin bacci na farko da kuma na biyu. A matakin farko ne mutum yake samun damar yin mafarki, a inda kwakwalwa ke aike wa da gabobin Dan Adam da sako ta yadda idan yana yin bacci zai iya motsawa duk inda yake so a kuma duk lokacin da ya gama.

ADVERTISEMENT

Saboda haka, a wannan lokaci na matakin bacci na farko (REM sleep), kwakwalwar na kashe mukunnin da ke kai wannan sako zuwa gabban mutum don gudun ka da ya yi hanzari ko gaggawar tashi ta kai shi ga jin ciwo ko rauni. Don haka, idan mutum ya zo tashi daga bacci, ya kamata kwakwalwar tasa ta gane cewa ya zo tashi, ta koma ta sake kunna makunnin wadannan gabbai nasa kafin ya kai ga tashin, amma a wasu lokutan sai a samu akasin haka kwakwalwar ta ki kunna wannan makunni, daga nan sai a samu akasi mutum ya kasa motsi ko yin numfashi har zuwa wasu dakikai ko ‘yan mintina kafin kwakwalwar ta gano cewa ta yi kuskure ba ta kunna ba, ta dawo ta sake kunna wannan mukunni.

Haka nan, a gargajiyance ana alakanta wannan matsala ta Dannau da Aljanin dare ko sharrin Mayu. Duk da cewa, yanayin da ake shiga kamar yadda a likitance aka bayyana iri daya ne, ta yadda mutum zai ji ya kasa numfashi ko motsi har zuwa wasu ‘yan dakikai ko mintina. Sannan, sau tari mutum ya kan ji jikinsa ya yi nauyi kamar an dora masa wani katon dutse ko an daddaure shi takamau; a cikin baccinsa ko ido biyu, wani lokacin ma wasu kan ce har shedanun ake gani ido kuru-kuru.

LABARAI MASU NASABA

Amfanin Ganyen Magarya Ga Lafiya Dan Adam

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaduwa Tsakanin Ma’aurauta

Wasu kuma na danganta wannan al’amari kai tsaye ga matsalar Mayu, ta yadda a cewarsu; ana ganin Mayen a daidai wannan lokaci, ko ya zo shi kadai ko kuma tare da wasu abokai ko ‘yan’uwansa; musamman idan ya kasance yana da wata matsala ko takun saka da wani. Ko kuma ya yi basaja ta hanyar zuwa a kamannin wani dan’uwanka ko wanda ka sani don ya hada ka gaba da shi ko gudun ka da ka ramfo shi.

Dannau
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Amfanin Ganyen Magarya Ga Lafiya Dan Adam
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Yadda Ciwon Hanta Ke Yaduwa Tsakanin Ma’aurauta
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Sake Daukar Shettima Da Tinubu Ya Yi Zai Kara Karfafa APC A Zaben 2027 –Farfesa Yerima
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Shugaban Rundunar Sojojin Nijeriya Ya Nemi Haɗin Kan Fararen Hula

MASU ALAKA

Amfanin Ganyen Magarya Ga Lafiya Dan Adam
Kiwon Lafiya

Amfanin Ganyen Magarya Ga Lafiya Dan Adam

July 25, 2026
Yadda Ciwon Hanta Ke Yaduwa Tsakanin Ma’aurauta
Kiwon Lafiya

Yadda Ciwon Hanta Ke Yaduwa Tsakanin Ma’aurauta

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Kiwon Lafiya

Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina

July 11, 2026
Next Post
’Yan Wasan Kasar Sin Sun Zarce Tsammani A Hangzhou 

’Yan Wasan Kasar Sin Sun Zarce Tsammani A Hangzhou 

LABARAI MASU NASABA

Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

Sin Za Ta Ci Gaba Da Ingiza Kyakkyawan Yanayin Cinikayya Tsakaninta Da Nahiyar Afirka

July 27, 2026
Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

Sakamakon Dangantakar Sin Da Afrika Na Taba Mutane Masu Rauni Da Karamin Karfi

July 27, 2026
Dannau

WAFU B 2026: Nijeriya Ta Doke Ghana Da Ci 4-2 A Wasan Farko

July 27, 2026
An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

An Samu Karin Sabbin Abubuwa Da Sin Ke Fitar Wa Waje Da Ake Wa Lakabi Da “New New Three”

July 27, 2026
Dannau

NSCDC Ta Cafke Mutane 2 Da Ake Zargi Da Sace Kayan Titin Jirgin Kasa A Kano

July 27, 2026
Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

Saura Kwanaki 100 A Bude CIIE Karo Na 9

July 27, 2026
Dannau

Obi-Kwankwaso Obasanjo Yake Goyon Baya, Amma Atiku Zai Iya Lashe Zabe – Momodu

July 27, 2026
Ribar Manyan Kamfanonin Sarrafa Kayayyaki Na Sin Ta Karu Da Kaso 18.7 A Rabin Farkon Bana

Ribar Manyan Kamfanonin Sarrafa Kayayyaki Na Sin Ta Karu Da Kaso 18.7 A Rabin Farkon Bana

July 27, 2026
Xi: Sin Ta Shirya Kara Karfafa Dangantaka Da Brazil

Xi: Sin Ta Shirya Kara Karfafa Dangantaka Da Brazil

July 27, 2026
Tinubu Ya Goyi Bayan Kafa Sabon Asibitin Koyarwa A Bichi — Ɗan Majalisar Kano

Tinubu Ya Goyi Bayan Kafa Sabon Asibitin Koyarwa A Bichi — Ɗan Majalisar Kano

July 27, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.