ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abubuwan Da Ya Kamata A Sani Game Da Dannau

by Sani Anwar
3 years ago

A likitance ana kiran Dannau da (sleep paralysis), a gargajiyance kuma ana kiran sa da Aljanin dare. A nan wani yanayi da mutum yake samun kansa a yayin bacci ko a farke, ta hanyar da mutum yana ji yana gani ya kasa yin numfashi ko motsi. A irin wannan lokaci, wasu har gane-gane suke yi barkatai; shi ya sa ake alakanta al’amarin da shedanu ko Mayu da sauran makamantansu.

Bugu da kari, duk a cikin mutum goma; akalla ana samun mutum hudu da ke shiga cikin irin wannan yanayi lokaci zuwa lokaci, sannan duk wanda ya samu kansa a wannan yanayi, ba ya wuce wasu ‘yan dakiku ko mintuna kafin ya samu kansa ko ya dawo hayyacinsa.

  • Hisbah Ta Yi Wa Mutum 4,000 Rajista Da Ke Son Gwamnatin Kano Ta Aurar Da Su
  • Duk Da Hukuncin Kotu, Gwamna Yusuf Ya Amince Da Kashe Naira Biliyan 3 Kan Ayyuka

Har ila yau, wannan yanayi da yake da alaka da Dannau, kamar yadda likitoci suka bayyana, yana faruwa ne sakamakon yadda baccin kowane Dan Adam ya rabu zuwa gida biyu, wanda a turance ake kira da ‘REM sleep’ da kuma ‘Non REM sleep’, ma’ana matakin bacci na farko da kuma na biyu. A matakin farko ne mutum yake samun damar yin mafarki, a inda kwakwalwa ke aike wa da gabobin Dan Adam da sako ta yadda idan yana yin bacci zai iya motsawa duk inda yake so a kuma duk lokacin da ya gama.

ADVERTISEMENT

Saboda haka, a wannan lokaci na matakin bacci na farko (REM sleep), kwakwalwar na kashe mukunnin da ke kai wannan sako zuwa gabban mutum don gudun ka da ya yi hanzari ko gaggawar tashi ta kai shi ga jin ciwo ko rauni. Don haka, idan mutum ya zo tashi daga bacci, ya kamata kwakwalwar tasa ta gane cewa ya zo tashi, ta koma ta sake kunna makunnin wadannan gabbai nasa kafin ya kai ga tashin, amma a wasu lokutan sai a samu akasin haka kwakwalwar ta ki kunna wannan makunni, daga nan sai a samu akasi mutum ya kasa motsi ko yin numfashi har zuwa wasu dakikai ko ‘yan mintina kafin kwakwalwar ta gano cewa ta yi kuskure ba ta kunna ba, ta dawo ta sake kunna wannan mukunni.

Haka nan, a gargajiyance ana alakanta wannan matsala ta Dannau da Aljanin dare ko sharrin Mayu. Duk da cewa, yanayin da ake shiga kamar yadda a likitance aka bayyana iri daya ne, ta yadda mutum zai ji ya kasa numfashi ko motsi har zuwa wasu ‘yan dakikai ko mintina. Sannan, sau tari mutum ya kan ji jikinsa ya yi nauyi kamar an dora masa wani katon dutse ko an daddaure shi takamau; a cikin baccinsa ko ido biyu, wani lokacin ma wasu kan ce har shedanun ake gani ido kuru-kuru.

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Wasu kuma na danganta wannan al’amari kai tsaye ga matsalar Mayu, ta yadda a cewarsu; ana ganin Mayen a daidai wannan lokaci, ko ya zo shi kadai ko kuma tare da wasu abokai ko ‘yan’uwansa; musamman idan ya kasance yana da wata matsala ko takun saka da wani. Ko kuma ya yi basaja ta hanyar zuwa a kamannin wani dan’uwanka ko wanda ka sani don ya hada ka gaba da shi ko gudun ka da ka ramfo shi.

Dannau
Sani Anwar
+ postsBio
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Gwamnati Ta Amince Da Inganta Cibiyar Kula Da Saran Maciji A Gwambe
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    ASUU Na Barazanar Shiga Yajin Aiki A Jami’o’in Jihohi 11 Kan Rashin Biyan Alawus-alawus
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Hukumar NDLEA Ta Lalata Sama Da Tan 12 Na Miyagun Ƙwayoyi A Kano
  • Sani Anwar
    https://hausa.leadership.ng/author/sani-anwar/
    Tattalin Arziƙin Ƙasa: Masana Sun Buƙaci Tinubu Ya Yi Hattara Da Shawarar IMF

MASU ALAKA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)
Kiwon Lafiya

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (2)

June 20, 2026
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)
Kiwon Lafiya

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir
Kiwon Lafiya

Yadda Gidajen Abinci Ke Wasa Da Rayuwar Al’umma Ta Amfani Da Ruɓaɓɓen Tumatir

May 30, 2026
Next Post
’Yan Wasan Kasar Sin Sun Zarce Tsammani A Hangzhou 

’Yan Wasan Kasar Sin Sun Zarce Tsammani A Hangzhou 

LABARAI MASU NASABA

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

Wakiliyar Sin Ta Bayyana Matsayar Kasar Yayin Taron Muhawarar Gaggawa Dangane Da Sudan

July 7, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Nuna Damuwa Kan Yawaitar Hare-haren Da Ake Kai Wa Jami’an Soji

July 7, 2026
Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Kan Ayyukan Rigakafin Ambaliyar Ruwa Da Karfafa Ceton Jama’a

July 7, 2026
Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

Gwamnonin APC Na Ganawar Sirri A Birnin Kebbi

July 7, 2026
An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

An Kai Kayayyakin Jin Kai Na Gaggawa Na Farko Da Gwamnatin Sin Ta Samar Wa Venezuela

July 7, 2026
Kotu Ta Umarci A Kamo Mata Dogarin Gwamna El-Rufa’i

MURIC Ba Ta Gamsu Da Rahoton Lafiyar El-Rufai Da Aka Gabatar A Kotu Ba

July 7, 2026
Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

Gwamnatin Neja Ta Sanya Dokar Hana Fita Bayan Mutane 80 Sun Rasu Sakamakon Rikicin Ƙabilanci

July 7, 2026
Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

Iran Ta Harba Wa Jiragen Ruwa Makamai Masu Linzami A Mashigar Hormuz

July 7, 2026
Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

Hukuma Ta Tilasta Wa Alƙali Yin Ritaya Saboda Karɓar Cin Hanci A Kano

July 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.