• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ACF Ta Nemi Rundunar Soji Ta Sake Dabarun Yakinta, Bayan Luguden Wutar Silame

by Khalid Idris Doya
6 months ago
in Labarai
0
ACF Ta Nemi Rundunar Soji Ta Sake Dabarun Yakinta, Bayan Luguden Wutar Silame
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Dattawan Arewa (ACF), ta bukaci sojojin Nijeriya da su sake duba dabarbaru da hikimomin da suke bi wajen magance matsalolin tsaro a arewacin kasar da ma Nijeriya baki daya.

A wata sanarwar da jami’in watsa labarai na kungiyar, Farfesa Tukur Muhammad Baba, ya fitar a ranar Litinin, ACF ta nuna damuwarta kan yadda ake samun ‘yan kura-kurai a aikace-aikacen sojojin.

Kungiyar ta nuna takaici kan yadda jirgin yakin sojoji ya yi luguden wuta a wasu kauyuka biyu a karamar hukumar Silame a Jihar Sakkwato a ranar Laraba, 25 ga watan Disamban 2024.

Harin wanda ya janyo mutuwar fafaren hula goma da jikkata wasu da dama.

Kungiyar Dattawan Arewan ta yaba wa gwamantin tarayya da gwamnan Jihar Sakkwato, Ahmed Aliyu bisa hanzarin kai dauki da daukan nauyin jinyar wadanda suka raunata tare da bata wani lokaci ba.

Labarai Masu Nasaba

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

“ACF ta kadu sosai da wannan lamarin na Silame, abun ya yi yawa a kasar nan. Irin wannan harin ya faru a kauyen Tudun Biri da ke Jihar Kaduna da Jihar Adamawa da Nasarawa, da jikkata mutane da dama wanda har yanzu muna fama da wadannan radadin a zukatanmu.”

A cewarsa sanarwar, kungiyar a kowani lokaci tana karfafa gwiwar hukumomin tsaro wajen yaki da kowace nauyin ta’addanci a fadin kasar nan, amma ba hakan ba ne zai ba su damar kashe fafaren hula ba tare da sun ji ko sun gani ba.

“Babu wanda ya isa ya shiga shakku game da irin wannan goyon bayan namu, kuma ACF ta yi kira ga duk wani mai kishin kasa a Nijeriya da ya ba jami’an tsaro goyon baya. Abu ne kawai da ba za a yarda da shi ba a bar ‘yan ta’adda da masu aikata laifuka na kowane irin launi su rike al’umma don neman kudin fansa ta hanyar ayyukansu na kiyayya.

“Wannan, abubuwan da suka faru irinsu na Silame da sauran wadanda suka faru kafin shi da kuma kididdigar tasirinsu ga ‘yan kasa marasa laifi suna daukar wani tsari mafi tayar da hankali tare da asarar Dan’adam wanda ba za a yarda da shi ba.”

Daga bisani kungiyar ta yi kira ga sojojin da su maida hankali wajen gudanar da ayyukansu bisa kwarewa da sanin ya kamata domin kauce wa faruwar irin wannan lamarin a nan gaba ta hanyar duba dabarun da hikimomin yaki da suke yi wajen kai farmakisu ga ‘yan ta’adda.

Kungiyar Dattawan Arewan ta kuma nemi masu hannu da shuni da kungiyoyi da su kai agaji da tallafi ga wadanda lamarin ya shafa domin rage musu radadin halin da suke ciki.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Arewa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Ta Karɓi Bashin Dala Biliyan 1.5 Daga Bankin Duniya Bayan Cire Tallafin Mai

Next Post

Manyan Batutuwa 10 Da Suka Mamaye Siyasar Nijeriya A 2024

Related

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano
Labarai

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

8 hours ago
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

10 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

10 hours ago
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara
Manyan Labarai

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

12 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

17 hours ago
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

18 hours ago
Next Post
Manyan Batutuwa 10 Da Suka Mamaye Siyasar Nijeriya A 2024

Manyan Batutuwa 10 Da Suka Mamaye Siyasar Nijeriya A 2024

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.