ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, September 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ACF Ta Nemi Rundunar Soji Ta Sake Dabarun Yakinta, Bayan Luguden Wutar Silame

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Acf

Kungiyar Dattawan Arewa (ACF), ta bukaci sojojin Nijeriya da su sake duba dabarbaru da hikimomin da suke bi wajen magance matsalolin tsaro a arewacin kasar da ma Nijeriya baki daya.

A wata sanarwar da jami’in watsa labarai na kungiyar, Farfesa Tukur Muhammad Baba, ya fitar a ranar Litinin, ACF ta nuna damuwarta kan yadda ake samun ‘yan kura-kurai a aikace-aikacen sojojin.

Kungiyar ta nuna takaici kan yadda jirgin yakin sojoji ya yi luguden wuta a wasu kauyuka biyu a karamar hukumar Silame a Jihar Sakkwato a ranar Laraba, 25 ga watan Disamban 2024.

ADVERTISEMENT

Harin wanda ya janyo mutuwar fafaren hula goma da jikkata wasu da dama.

Kungiyar Dattawan Arewan ta yaba wa gwamantin tarayya da gwamnan Jihar Sakkwato, Ahmed Aliyu bisa hanzarin kai dauki da daukan nauyin jinyar wadanda suka raunata tare da bata wani lokaci ba.

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sanya Tsadar Man Fetur Ke Ci Gaba Da Shafar Nijeriya — Dangote

NSCDC Ta Kama Ɓarayin Mota, Ta Ƙwato AK-47 A Abuja

“ACF ta kadu sosai da wannan lamarin na Silame, abun ya yi yawa a kasar nan. Irin wannan harin ya faru a kauyen Tudun Biri da ke Jihar Kaduna da Jihar Adamawa da Nasarawa, da jikkata mutane da dama wanda har yanzu muna fama da wadannan radadin a zukatanmu.”

A cewarsa sanarwar, kungiyar a kowani lokaci tana karfafa gwiwar hukumomin tsaro wajen yaki da kowace nauyin ta’addanci a fadin kasar nan, amma ba hakan ba ne zai ba su damar kashe fafaren hula ba tare da sun ji ko sun gani ba.

“Babu wanda ya isa ya shiga shakku game da irin wannan goyon bayan namu, kuma ACF ta yi kira ga duk wani mai kishin kasa a Nijeriya da ya ba jami’an tsaro goyon baya. Abu ne kawai da ba za a yarda da shi ba a bar ‘yan ta’adda da masu aikata laifuka na kowane irin launi su rike al’umma don neman kudin fansa ta hanyar ayyukansu na kiyayya.

“Wannan, abubuwan da suka faru irinsu na Silame da sauran wadanda suka faru kafin shi da kuma kididdigar tasirinsu ga ‘yan kasa marasa laifi suna daukar wani tsari mafi tayar da hankali tare da asarar Dan’adam wanda ba za a yarda da shi ba.”

Daga bisani kungiyar ta yi kira ga sojojin da su maida hankali wajen gudanar da ayyukansu bisa kwarewa da sanin ya kamata domin kauce wa faruwar irin wannan lamarin a nan gaba ta hanyar duba dabarun da hikimomin yaki da suke yi wajen kai farmakisu ga ‘yan ta’adda.

Kungiyar Dattawan Arewan ta kuma nemi masu hannu da shuni da kungiyoyi da su kai agaji da tallafi ga wadanda lamarin ya shafa domin rage musu radadin halin da suke ciki.

Acf
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Dangote
Manyan Labarai

Dalilin Da Ya Sanya Tsadar Man Fetur Ke Ci Gaba Da Shafar Nijeriya — Dangote

September 15, 2026
NSCDC Ta Kama Ɓarayin Mota, Ta Ƙwato AK-47 A Abuja
Labarai

NSCDC Ta Kama Ɓarayin Mota, Ta Ƙwato AK-47 A Abuja

September 15, 2026
Gwamnatin Zamfara Za Ta Mayar Da Yara 453,602 Makaranta
Labarai

Gwamnatin Zamfara Za Ta Mayar Da Yara 453,602 Makaranta

September 15, 2026
Next Post
Manyan Batutuwa 10 Da Suka Mamaye Siyasar Nijeriya A 2024

Manyan Batutuwa 10 Da Suka Mamaye Siyasar Nijeriya A 2024

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sanya Tsadar Man Fetur Ke Ci Gaba Da Shafar Nijeriya — Dangote

September 15, 2026
Xi Ya Bukaci ‘Yan Sandan Sin Su Ci Gaba Da Dukufa Ga Hidimta Wa Jama’a Tare Da Sauke Nauyi Da Nuna Sadaukarwa

Xi Ya Bukaci ‘Yan Sandan Sin Su Ci Gaba Da Dukufa Ga Hidimta Wa Jama’a Tare Da Sauke Nauyi Da Nuna Sadaukarwa

September 15, 2026
NSCDC Ta Kama Ɓarayin Mota, Ta Ƙwato AK-47 A Abuja

NSCDC Ta Kama Ɓarayin Mota, Ta Ƙwato AK-47 A Abuja

September 15, 2026
Gwamnatin Zamfara Za Ta Mayar Da Yara 453,602 Makaranta

Gwamnatin Zamfara Za Ta Mayar Da Yara 453,602 Makaranta

September 15, 2026
’Yan Ta’adda Sun Kai Wa Ƙauyuka 2 Hari A Adamawa

Boko Haram Sun Kashe Mutane 4 Tare Da Ƙone Gidaje A Adamawa

September 15, 2026
Wani Mutum Ya Kashe Kishiyar Mahaifiyarsa A Kogi

’Yan Ta’adda Na Shirin Kai Hare-Hare Makarantu, Wuraren Ibada Da Sansanonin NYSC – ’Yansanda

September 15, 2026
Gwamnatin Sakkwato Ta Rufe Masallacin Sheikh Lukuwa Bayan Harin Da Aka Kai Masa

Gwamnatin Sakkwato Ta Rufe Masallacin Sheikh Lukuwa Bayan Harin Da Aka Kai Masa

September 15, 2026
Hannun Jari: Dangote Ya Yi Wa ’Yan Nijeriya Alƙawarin Samun Gaggwaɓar Riba

Hannun Jari: Dangote Ya Yi Wa ’Yan Nijeriya Alƙawarin Samun Gaggwaɓar Riba

September 15, 2026
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Arziƙin Dangote Ya Haura Dala Biliyan 50 Bayan Fara Sayar Da Hannun Jarin Matatarsa – Forbes

September 15, 2026
Jawabin Xi A Taron BRICS, Mafita Ce Ga Matsalolin Duniya

Jawabin Xi A Taron BRICS, Mafita Ce Ga Matsalolin Duniya

September 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.